Aminiya:
2025-03-25@14:00:22 GMT

Gwamnatin Filato ta dakatar da haƙar ma’adinai saboda matsalar tsaro

Published: 21st, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, ya bayar da umarnin dakatar haƙar ma’adanai a faɗin jihar daga ranar 21 ga watan Fabrairu, 2025.

Ya yanke wannan shawara ne saboda ayyukan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida wanda ke da alaƙa da laifuka da suka shafi ta’addanci, satar mutane, da fataucin miyagun ƙwayoyi.

Najeriya ta taɓarɓare bayan mulkin IBB – Peter Obi Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu

Haka kuma, ya ce yawan baƙi da ke shiga yankunan da ake haƙar ma’adanai na ƙara haddasa matsalar tsaro.

“Akwai ƙaruwar ayyukan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba, wanda ke haifar da matsalolin tsaro a sassa daban-daban na jihar.

“Haka kuma, yawan baƙin da ke shiga yankunan haƙar ma’adanai na ƙara yawan laifuka kamar ta’addanci, garkuwa da mutane, da fataucin miyagun ƙwayoyi,” in ji Gwamna Mutfwang.

Domin shawo kan wannan matsala, gwamnatin ta kafa kwamitin da zai binciki waɗanda ke da izinin haƙar ma’adanai da kuma ƙirƙirar tsarin kula da ayyukan haƙar.

Gwamnan ya ƙara da cewa za su yi aiki tare da Gwamnatin Tarayya domin tabbatar da tsare-tsaren doka da kuma inganta matakan tsaro.

“Za mu haɗa kai da Gwamnatin Tarayya domin bitar yadda ake sanya ido kan ayyukan haƙar ma’adanai.

“Haka kuma, za mu tabbatar da cewa kamfanonin haƙar suna bai wa al’umma gudunmawa,” in ji shi.

Gwamnan ya yi alƙawarin duba matsalar tsaro a yankunan da ake haƙar ma’adanai gaba ɗaya tare da tabbatar da cewa kamfanonin haƙar ma’adanai suna taimaka wa al’ummomin yankunan da suke aiki a cikinsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Caleb Muftwang gwamna Haƙar Ma adanai matsalar tsaro haƙar ma adanai ayyukan haƙar

এছাড়াও পড়ুন:

Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi

Sai dai duk da yaba wa Amurka bisa irin taimakon da ta bayar a baya, Byanyima ta nuna damuwa kan yadda aka dakatar da tallafin kwatsam ba tare da shiri ba.

Wannan na iya haddasa koma baya a ƙoƙarin da aka shafe shekaru ana yi na rage yawan masu kamuwa da cutar, musamman a yankunan da ke fama da talauci da ƙarancin kayan kiwon lafiya.

Masana kiwon lafiya sun bayyana cewa, idan ba a samu sabbin hanyoyin tallafi ba, yiwuwar ƙaruwar mace-mace sakamakon cutar HIV na da matuƙar girma.

Hakan na iya rusa nasarorin da aka samu a yaƙin da duniya ke yi da cutar.

Ana ci gaba da kira ga ƙasashen duniya da ƙungiyoyin agaji da su ceto shirin da ke kare miliyoyin rayuka daga barazanar cutar HIV.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Ɗauko Sojoji Daga Waje Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • An Ɗauko Sojoji Daga Wajen Don Horas Da Dakarun Nijeriya 
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi
  • Gwamnonin PDP sun garzaya Kotun Ƙoli kan dakatar da Gwamnan Ribas
  • UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
  • Gwamnonin Arewa sun yi wa Radda ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Dakatar da Gwamnan Ribas zubar da ƙimar Nijeriya ne a idon duniya — Jonathan