HausaTv:
2025-02-22@22:18:38 GMT

Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa

Published: 22nd, February 2025 GMT

Bayan shekaru 47, Faransa ta janye daga sansanin sojinta mafi girma a kasar Ivory Coast

A hukumance Faransa ta mayarwa kasar Ivory Coast babban sansanin soji da ta mamaye kusan shekaru hamsin a kusa da birnin Abidjan, a wani bangare na yarjejeniyar da kasashen biyu suka kulla.

Filin tashar jiragen ruwa na Port Bouet, wanda ke dauke da bataliyar sojoji na 43 da na ruwa, ya shaida bikin mika ta, inda aka daga tutar Ivory Coast a farfajiyar sansanin, kuma an canza sunan ta da sunan babban hafsan soji na farko a Ivory Coast, Thomas Dakine Ouattara, wanda hakan ya kawo karshen kasancewar Faransa a kasar tun shekarar 1978.

Ministan tsaron kasar Ivory Coast, Tene Berahima Ouattara, ya jaddada cewa: Wannan mataki na wakiltar wani sabon mataki na dangantakar abokantaka da hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tsakanin kasashen biyu. A nasa bangaren, ministan tsaron kasar Faransa Sébastien Lecornu ya bayyana cewa: “Duniya tana canjawa, kuma a fili yake cewa dole ne dangantakar kasashen biyu ta bunkasa,” yana mai nuna alfaharinsa ga “dangantakar da aka gina bisa abota da kwarewa tsakanin Faransa da Ivory Coast.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Ivory Coast

এছাড়াও পড়ুন:

 Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta

Jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah sayyid Ali Khamnei wanda ya gana da sarkin Katar  a jiya Laraba ya bayyana cewa; Siyasar Iran ta ginu ne akan kyautata alaka da kasashen makwabta, kuma tuni an cimma sabbin matakai a wannan fagen.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya kuma fada wa sarkin na Katar Tamim Bin Hamad ali-Sani cewa, ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci yana fadi tashi a wannan fagen na kyautata alaka da kasashen makwabta, tare da yin kira da cewa yarjeniyoyin da aka kulla su zama masu kare maslahar kasashen biyu.

Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya bayyana kasar Katar a matsayin kasa abokiya, kuma ‘yar’uwa ta Iran, duk da cewa har  yanzu da akwai wasu batutuwa da ba a kai ga warware sub a,kamar dawo da kudaden Iran da aka zuba a Bankunan kasar daga Korea Ta Kudu.

A nashi gefen sarkin Katar ya jinjinawa matakan da Iran din take dauka na taimakawa raunana a duniya, da kuma al’ummar Falasdinu, kuma yadda ta kasance a tare da Falasdinawa wani abu ne da ba za taba mancewa da shi ba har abada.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani mutum ya yi wa agolarsa fyaɗe ta samu juna biyu
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitulmalin Amurka
  • Hamas Ta Mika Fursinonin HKI 6 Sannan Tana Dakon A Shiga Marhala Ta Biyu
  • Sojojin Ruwa Da Kuma Sojijin Sama Na JMI Sun Hada Guiwa Don Yin atisaye Tare Mai taken Zulfikar
  • Yake-Yaken Kasa Da Kasa Ne Suka Mamaye Taron G20 Na Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar A Afirka Ta Kudu
  • Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Jaddada Rashin Amincewarta Da Mika Kan Kasar Ga Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sojojin Gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Luguden Wuta Kan Gabar Yammacin Kogin Jordan
  • Jakadan Sin Dake Najeriya Ya Gana Da Karamar Ministar Harkokin Wajen Kasar
  •  Jagora: Siyasar Kasar  Iran  Ta Ginu Ne Akan Kyautata Alaka Da Kasashen Makwabta