‘Yan Bindiga Sun Kashe Wani Mutum Tare Da Sace Mutum Biyu A Kaduna
Published: 23rd, February 2025 GMT
“Duk da cewa an dan samu raguwar kai hare-hare amma har yanzu ana samun wasu su shiga su kashe mutane sannan su tafi da wasu domin kuɗin fansa” in ji ɗan majalisar.
Sannan ya kuma kalubalanci rashin hanya mai kyau a yankunan wanda a cewarsa hakan ma yana kawo tsaiko wajen fatattakar yan ta’adda.
Danlami Stingos ya kuma yabi gwamnatin jihar Kaduna bisa kokarin da take yi na yaƙi da yan ta’adda sannan ya kuma riko gwamnatin da ta dage wajen samar da hanyoyi a yankunan da suke fama da hare-haren ‘yan bindiga.
কীওয়ার্ড: Garkuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Uba Sani, ya naɗa Sarkin Kauru, Mai Martaba Alhaji Ya’u Shehu Usman, a matsayin Amirul Hajj kuma jagoran tawagar jami’an jihar don aikin Hajjin 2025.
A cikin wata sanarwa, Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Ibraheem Musa, ya bayyana cewa naɗin wannan basarake mai daraja ya biyo bayan sadaukarwarsa, da gaskiya, da jagorancinsa, da nagarta a harkokin mulki.
A matsayinsa na Amirul Hajj, Sarkin zai yi aiki kafada da kafada da Kwamitin Hajj na Musamman na Jihar Kaduna tare da haɗin gwiwa da hukumomin Jiha, Tarayya, da na ƙasashen duniya, domin tabbatar da aikin Hajji cikin nasara ga maniyyatan Jihar Kaduna.
Gwamnan ya kuma yi addu’a ga Allah da ya ma Sarkin jagora da kariya yayin gudanar da wannan muhimmin aiki.
Safiyah Abdulkadir