Tawagar Iran a Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa: Ba a hana sayar da jirgin mara matuki ciki na ‘Shahed’ ba

Tawagar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya ta mayar da martani kan baje kolin jirgin saman Iran a babban taron jam’iyyar Republican inda ta ce: Babu wata doka da ta haramta sayar da jirgin sama maras matuki ciki na Shahed.

Jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya kara da cewa: Jirgin sama mara matuki ciki na Shahed yana daya daga cikin mafi kyawun nau’ikan jiragen sama marasa matuka ciki a duniya, kasancewar yana da kwarewa sosai wajen ganowa, sa ido da kuma aiwatar da aiki inda ya dace, sannan kuma yana da araha da rahusa.

Jakadan Jamhuriyar Musulunci ta Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya ci gaba da cewa: Babu wani haramcin sayar da jirgin a doka, kuma duk wata kasa da ta yi alkawarin ba za ta yi amfani da shi ba wajen kai wa wata kasa hari, tana iya neman sayan jirgin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Iran a Majalisar Dinkin Duniya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar

Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin kafa sashen kula da masu fama da matsalar kwakwalwa a jihar ya zama doka.

Dokar za ta samar da kariya da kuma bunkasa ‘yancin masu fama da matsalar kwakwalwa musamman masu tu’ammuli da muggan kwayoyi a fadin jihar Kaduna.

Da yake jagorantar zaman majalisar, shugaban majalisar dokokin jihar kaduna, Yusuf Dahiru Liman ya sanar da amincewa da kudirin wanda aka yiwa lakabi da kudirin kula da lafiya masu fama da cutar kwakwalwa na jihar Kaduna.

Da yake gabatar da rahoto, shugaban kwamitin hadin gwiwa na lafiya da sharia, wanda aka dorawa alhakin yin nazari a kan wannan kudiri, Mr. Haruna Barnabas ya ce sun yi nazarin kudirin sannan sun gano cewa akwai bukatar a karfafa matakan da jihar ke bi wajen kula da masu fama da matsalar kwakwalwa domin bunkasa lafiyar kwakwalwa da magance kalubalen da masu tu’ammuli ke fuskanta a cikin al’umma.

Ya ce sabuwar dokar za ta taimaka wajen sauya suna tare da manufofin Hukumar Yaki da Tu’ammuli da Muggan Kwayoyi ta Jihar Kaduna-KADBUSA zuwa Hukumar Yaki da Tu’ammuli da Muggan Kwayoyi da Kula da Lafiyar Kwakwalwa ta Jihar Kaduna-KADSAMHSA domin ya dace da yadda ake tafiyar da irin wadannan ayyuka a matakin duniya.

A cewar shugaban kwamitin, za ta tabbatar da cewa ana mutunta masu tu’ammuli da muggan kwayoyi, da gyara dabi’un su da kuma sake shigar da su cikin al’amuran al’umma don su bada gudunmuwa mai ma’ana.

A wani labarin kuma, majalisar dokokin jihar Kaduna ta mika wani kudiri dake bukatar kafa Hukumar Kula da Ilimin Manyan Makarantun Sakandare, na 2025.

Kudirin, wanda dan majalisa mai wakiltar birnin Zaria a majalisar dokokin jihar Kaduna, Barrister Mahmud Lawal Isma’ila ya ce kudirin zai inganta tsarin ilimin jihar ya dace da ci gaban zamani.

Ya ce idan aka amince da kudirin ya zama doka, hukumar za ta rika kula da dukkanin manyan makarantun sakandare a fadin jihar, don tabbatar da ganin ana sarrafa kudaden da aka ware ma bangaren ilimi don ganin ya habbaka.

Shamsuddeen Mannir Atiku

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran Ya Ce: Iran Ba Ta Kallon Tattaunawan Iran Da Amurka A Matsayin Kawo Karshen Takaddama A Tsakaninsu
  • Ina Dalilin Da Ya Sa Cinikin Shige Da Fice Na Kasar Sin Ke Samun Bunkasuwa Mai Dorewa Ba Tare Da Tangarda Ba?
  • Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
  • Sojojin Yemen Sun Kakkabo Jirgin Yakin Amurka Wanda Ake Sarrafa Shi Daga Nesa Na 19
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Dakatar Da Matakin Kare-Karen Harajin Fito Kan Hajojin Da Ake Shigarwa Kasar
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman