Magoya Bayan Tottenham Sun Yi Zanga-Zanga
Published: 23rd, February 2025 GMT
Sama da magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Tottenham 1,000 ne suka yi zanga-ganga kan shugaban kungiyar, Daniel Leby kafin wasa da Manchester United a Premier ranar Lahadin da ta gabata. An yi ta kuwa da cewar ”Leby ya bar kungiyar da kuma ”Enic ya bar Tottenham” yayin da magoya baya suka rinka daga tuta a kusa da filin wasa, wadanda ke kiraye-kirayen a kawo canji.
An kuma tsara yin zaman dirshan da zarar an tashi wasan Premier a karawa da United, inda magoya baya suka bukaci da kowa ya tsaya a filin wasan Tottenham. An kafa kyalle a wajen zaman masu gida da wajen zaman baki da aka rubuta sakon cewar ”lokacin canji ya yi” domin ”shekara 24 an sauya masu horarwa 16 da lashe kofi daya.”
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Rufe Gasawar Wasannin Hunturu Ta Asiya Karo Na 9 Babbar Gasar Wasannin Kankara Ta Zama Damar Tabbatarwa Duniya Niyyar Karfafa Zaman LafiyaKafin Tottenham ta buga wasa da Manchester United ranar Lahadi tana ta 15 a teburi, wadda ta ci wasa daya daga takwas baya da ta fafata. Tottenham ta lashe League Cup a 2008 – tun bayan da Leby da Enic suka mallaki kungiyar daga Sir Alan Sugar, kusan shekara 25 da ta wuce. To sai dai Tottenham ita ce kan gaba a samun riba a Premier League a tsawon shekarun, inda Leby ya samar da £1.2bn da aka gina katafaren filin wasa da kasaitaccen wajen atisaye.
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bukaci Hanzarta Hukunta Shugabannin ‘Yan Sahayoniyya Kan Laifukan Da Suka Aikata
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya yi kira da a gaggauta bibiyar bayanan manyan laifuka na shugabannin gwamnatin mamayar Isra’ila
A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na kasar Holland, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi Allah wadai da ci gaba da mamaya da kuma laifukan da yahudawan sahayoniyya suke yi a Falasdinu, tare da yin kira ga kasashen duniya da su dauki matakin gaggawa wajen hanzarta bibiyar bayanan shari’a da laifuka a kotunan duniya dangane da kisan kiyashi da laifukan yaki da shugabannin mamayar Isra’ila suka aikata.
Kamfanin dillancin labaran Fars ya habarta cewa: Ministan harkokin wajen kasar Holand Caspar Veldkamp da takwaransa na Iran Abbas Araqchi sun tattauna kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu da ci gaban kasa da kasa a wata tattaunawa ta hanyar wayar tarho a jiya Asabar.
Haka nan kuma yayin da yake ishara da dogon tarihin dangantakar da ke tsakanin Iran da Netherlands, ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye ta ke ta gudanar da dukkanin harkokin da suka shafi kasashen biyu bisa mutunta juna da moriyarsu.