Jami’ar Sojoji ta BIU ta ƙaddamar da taron magance zamba
Published: 23rd, February 2025 GMT
Jami’ar Sojojin Nijeriya da ke Biu (NAUB) ta ƙaddamar da taron magance zamba ta hanyar binciken fasaha karo na farko, wanda ya nuna ƙaruwar tasirin wannan jami’a a fagen ilimi a Nijeriya.
Taron ya gudana ne bisa taken “Kididdigar Forensic: Zuwa Ga Sabon Tsarin Magance da Gano Zamba,” wanda Farfesa Ahmad Imam, ƙwararre a fannin ƙididdigar kuɗi da magance zamba ya gabatar.
Tattaunawar ta jaddada dabarun zamani domin tunkarar zamba mai salo da kuma tsare-tsaren da za su taimaka wajen gano da magance laifukan kuɗi da ke ƙara ƙamari.
Shugaban Jami’ar NAUB, Farfesa Kyari Mohammed, ya bayyana wannan taro a matsayin wani muhimmin mataki ga jami’ar.
A cewarsa: “Abin alfahari ne mu yi bikin wannan muhimmin taro na farko, wanda ke nuna jajircewar NAUB wajen habaka ilimi da warware matsalolin al’umma.”
Shugaban Kwamitin Shirya Taron, Farfesa Adamu Isa Harir, ya bayyana taron a matsayin wata al’ada mai cike da tarihi a fagen ilimi.
Ya ce: “Wannan taro ba wai kawai nasara ce ga jami’a ba, har ila yau, yana nuna muhimmancin bincike da kirkire-kirkire wajen kawo sauyi ga al’umma.”
Farfesa Ahmad Imam ya jaddada bukatar sabon salo wajen yakar zamba, tare da bayyana yadda zamani ke buƙatar sababbin hanyoyin daidaitawa da matsalolin laifukan kudi a duniya da ke sauyawa cikin sauri.
A jawabin godiya, Magatakardar Jami’ar, Birgediya Janar H.Y. Abdulhamid, ya gode wa dukkan wadanda suka bayar da gudunmawa wajen samun nasarar taron.
A cewarsa: “Muna matukar godiya da goyon bayan shugabannin jami’a da kuma kokarin ma’aikata wajen tabbatar da nasarar wannan taro.”
Haka kuma, Shugaban Sashen Kididdiga, Dakta S.J. Inyada, ya gabatar da kyauta ta musamman ga Farfesa Ahmad Imam a matsayin yabo kan gudunmawarsa a fannin kididdigar bincike ta hanyar fasahar zamani.
Dakta Inyada ya yaba wa Mataimakin Shugaban Jami’ar da shugabannin jami’a bisa jajircewarsu wajen inganta bincike da harkokin ilimi a jami’ar.
Wannan taro ba wai kawai ya zama wani babban ci gaba ga NAUB ba, har ila yau, ya tabbatar da alkawarin jami’ar na ci gaba da girmama bincike, kirkire-kirkire, da kawo sauyi mai ma’ana ga al’umma.
Wannan ya tabbatar da rawar NAUB a matsayin jagora wajen bunkasa bincike da ilimi a Nijeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jami ar Sojoji jihar Borno wannan taro
এছাড়াও পড়ুন:
An Bude Taron Shekara-Shekara Na Dandalin Tattauna Raya Kasa Na Sin Na 2025
A yau Lahadi ne aka bude taron shekara-shekara na dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin na 2025 a nan birnin Beijing, taron da cibiyar binciken raya kasa ta majalisar gudanarwar kasar Sin ta shirya tare da hadin gwiwar asusun binciken raya kasa na kasar Sin. Firaministan kasar Sin Li Qiang ya halarci bikin bude taron, inda ya gabatar da muhimmin jawabi, wanda a cikinsa ya jaddada aniyar kasar Sin ta kara bude kofa ga kasashen waje.
Shi ma mataimakin darektan ofishin kula da harkokin yau da kullum na hukumar kudi da tattalin arziki ta kwamitin kolin JKS Han Wenxiu, wanda ya halarci taron na shekara-shekara, ya ce kasar Sin za ta dauki dukkan matakai na habaka kashe kudi, da kuma ci gaba da haifar da yanayi, ta yadda ingantaccen ci gaba da kyakkyawar rayuwa za su rika karfafar juna.
Hajiya Safara’u, Mahaifiyar Gwamna Raɗɗa Ta Rasu An Kashe Askarawa 6 da ‘Yan Sa-kai 4 A ZamfaraZa a shafe kwanaki biyu ana gudanar da taron, bisa jigon “Ingiza karfin ci gaba, tare da inganta kyakkyawan ci gaban tattalin arzikin duniya”. Taron ya hallara wakilai daga manyan kamfanoni 86 na kasashe 21. A yayin taron, mahalarta na kasar Sin da na kasashen waje, za su gudanar da tarukan karawa juna sani 12, kan batutuwan da suka hada da manyan manufofi, da yin gyare-gyare, da kara yawan amfani da kayayyaki, da sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da fasahar AI.
Tun lokacin da aka kaddamar da dandalin tattauna raya kasa na kasar Sin a shekarar 2000, dandalin ya zama wata muhimmiyar gada da ta sa kaimi ga yaukaka tattaunawa, da hadin gwiwa tsakanin Sin da sauran kasashen duniya. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp