Sheikh Kassim: Gwagwarmaya Za Ta Ci Gaba Da Dukkanin Karfinta
Published: 23rd, February 2025 GMT
Babban sakataren kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasrallah Sheikh Na’im Kassim ya bayyana Shahidin al’umma Sayyid Hassan Nasrallah da cewa, jagora ne na musamman na al’ummun larabawa da musulmi kuma shugaban gwgawarmaya.
A cikin jawabin da ya gabatar a lokacin jana’izar Shahid Sayyid Hassan Nasrallah, da Shahid Hashim Safiyuddin, inda ya bayyan cewa: A wannan rana muna yin ban kwana da jagora na tarihi na musamman wanda kuma yake a matsayin alkiblar ‘yantattun na duniya.
Babban sakataren kungiyar ta Hizbullah Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Sayyid Shahid Hassan Nasrallah ya narke a cikin yi wa musulunci hidima da kuma a cikin riko da wilaya, ya kuwa yi shahada ne a sahun gaba na fagen daga, kuma zai ci gaba da zama a cikin zukatanmu da ruhinmu, za kuma mu yi riko da amana mu ci gaba da tafiya akan wannan tafarkin.
Shekih Na’im Kassim wanda ya yi Magana da sayyid Nasrallah, ya ce: Kai ne kake fadin cewa, tare za mu kammala wannan tafiyar,ko da kuwa za a kashe mu baki daya. Ya Sayyid Nasrallah muna nan akan wannan alkawalin.”
Sheikh Kassim ya kuma ce; Taron da aka yin a jana’iza, yana a matsayin bayyana ra’ayi ne akan riko da gwagwarmaya wanda irinsa ya yi karanci a tarihin Lebanon.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Sayyid Hassan Nasrallah
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
Wani babban jami’in Diblomasiyya na kasar Iran ya bada sanarwan cewa zagaye na biyu a tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka za’a gudanar da shi ne a kasashen Turai a ranar 19 ga watan Afrilun wannan shekara ta 2025.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto mataimakin ministan harkokin waje na JMI kan al-amuran da suka shafi siysa Majid Takht-Ravabchi yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake gabatarwa Majalisar dokokin kasar Iran rahoto kan taron tawagar Amurka da kuma JMI a birnin Mascat na kasar Omman a ranar Asabar da ta gabata.
Jami’in diblomasiyyar ya kara da cewa, a tattaunawar da ba kai tsaye ba tsakanin kasashen biyu a ranar Asabar da ta gabata yayin kokarin gano, wuri guda wanda zasu iya tsayawa a kansa don gina tattaunawar a kansa. Takht-Ravanchi ya nakalto tawagar gwamnatin Amurka na cewa da gaske suke a tattaunawar, kuma basa neman yaki da kasar Iran, banda haka a shirye suke su saurari korafe korafe gwamnatin JMI. A ranar Asabar da ta gabace ministan harkokin wajen kasar Amurka da wakilin kasar Amurka a harkokin gabas ta tsakiya Steve Witkoff suka gudanar da zagaye na farko a tsakanin kasashen biyu a birnin Mascat na kasar Omman. Tashar talabijin ta Al-Manar ta kasar Lebanon ta nakalto shafin yanar gizo na larabarai na Axion na fadar cewa taro nag aba zai kasance a birni Roma na kasar Italiya.