Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da tsawaita lokacin yin rajistar maniyyata zuwa Hajjin 2025 a Ƙasar Saudiyya har bayan Azumin Ramadan.

Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Sale Usman, ya bayyana hakan a wata hira da aka yi da shi a Abuja.

Farfesa Usman ya kuma bayyana cewa an rage naira biliyan 54 daga kudaden da masu ruwa da tsaki ke caji domin saukaka wa maniyyata wajen biyan kuɗin tafiya.

Ya tabbatar da cewa ana duba sabbin hanyoyin inganta muhimman ayyuka kamar abinci, masauki, da kula da lafiyar alhazai yayin da suke ƙasa mai tsarki.

A cewarsa, hukumar za ta ɗauki nauyin kuɗin tafiyar ƙwararrun masu dafa abinci 60 da za su sa ido kan shirye-shiryen abinci a wuraren da aka tanada, sakamakon korafe-korafen matsaloli da aka fuskanta a shekarar da ta gabata.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Maniyyata Ragewa Tsawaita Rajistar

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Taraba, SP Abdulahi Usman, ya rasu bayan fama da doguwar jinya.

Kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Olumuyiwa Adejobi ne, ya tabbatar da rasuwarsa cikin wata sanarwa a ranar Laraba.

’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa Ribas: Za mu ɗauki matakan da za su shafi tattalin arzikin Nijeriya — ’Yan ƙwadago

Ya bayyana Usman a matsayin jajirtaccen ɗan sanda kuma gada tsakanin jami’an tsaro da al’umma.

“SP Usman ya shafe shekaru uku yana ƙarfafa hulɗa tsakanin ’yan sanda da jama’ar Taraba.

“Ƙwarewarsa, mutuntaka da jajircewarsa wajen neman adalci sun an samu tasiri,” in ji Adejobi.

Ya ƙara da cewa rasuwar Usman babban rashi ne ga rundunar ’yan sanda, abokan aikinsa da duk wanda ya san shi.

Sashen hulɗa da jama’a na ’yan sanda ya miƙa ta’aziyya ga iyalansa da kuma ‘yan uwansa, tare da yin addu’ar Allah Ya masa rahama.

Za a ci gaba da tunawa da Usman saboda sadaukarwar a aikinsa da ƙoƙarinsa na kyautata hulɗa tsakanin ’yan sanda da al’umma a Jihar Taraba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisa ta buƙaci a rage kuɗin data don sauƙaƙa wa ’yan Najeriya 
  • Jagoran Juyin Musulunci Ya Amince Da Yin Afuwa Ga Wasu Fursunoni Masu Yawa
  • JIBWIS Ta Raba Kayan Abinci Na Kimanin Naira Miliyan 9 Ga Marayu
  • Kakakin ’yan sandan Taraba, Abdullahi Usman, ya rasu
  • Gwamnatin Kano za ta hukunta masu shigar banza a bikin Sallah
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
  • Ministan Lafiya Ya Yi Alƙawarin Inganta Tallafi Ga Likitoci A Hajjin 2025