Hajj 2025: NAHCON Ta Rage N54bn Daga Kudaden Cajin Maniyyata
Published: 24th, February 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da tsawaita lokacin yin rajistar maniyyata zuwa Hajjin 2025 a Ƙasar Saudiyya har bayan Azumin Ramadan.
Shugaban Hukumar, Farfesa Abdullahi Sale Usman, ya bayyana hakan a wata hira da aka yi da shi a Abuja.
Farfesa Usman ya kuma bayyana cewa an rage naira biliyan 54 daga kudaden da masu ruwa da tsaki ke caji domin saukaka wa maniyyata wajen biyan kuɗin tafiya.
Ya tabbatar da cewa ana duba sabbin hanyoyin inganta muhimman ayyuka kamar abinci, masauki, da kula da lafiyar alhazai yayin da suke ƙasa mai tsarki.
A cewarsa, hukumar za ta ɗauki nauyin kuɗin tafiyar ƙwararrun masu dafa abinci 60 da za su sa ido kan shirye-shiryen abinci a wuraren da aka tanada, sakamakon korafe-korafen matsaloli da aka fuskanta a shekarar da ta gabata.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Maniyyata Ragewa Tsawaita Rajistar
এছাড়াও পড়ুন:
Sabon Shugaban Kasar Gabon Ya Bayyana Shiransa Na Kawo Sauyi Mai Kyau A kasar
Bayan da hukumar zaben kasar Gabon ta tabbatar da nasarar da Brice Oligui yayi a zaben shugaban kasa na karshen makon da ya gabata, shugaban ya gabatar da jawabinsa na farko ga mutanen kasar, inda ya bayyana masu kan cewa, babu jin dadi sai tare da wahala.
Shafin tanar gizo na labarai ‘Africa News” ya nakalto shugaban yana cewa muhimman al-amuran da zai sa a gaban a shugabancin kasar sun hada da sauya tsarin tattalin arzikin kasar daga dogaro da man fetur zuwa harkokin kasuwanci, har’ila yau zai yaki cin hanci da rashawa.
Brice ya ce, ya zo ne a matsayin mai gina kasa, kuma yana son taimakon su don samun nasara a wannan gagarum,in aikin.
A ranar lahadin da ta gabata ce hukumar zaben kasar Gabaon ta bada sakamakon zaben shugaban kasa wanda aka gudanar a ranar Asabar wanda ya nuna cewa masu zabe a kasar sun zabi Brice a matsayin shugaban kasa tare da samun kasha 90.4% na yawan kuri’un da aka kada, kuma yawan mutanen da suka fito kara kuri’un ya kai kasha 74%.