Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Nemi Hadin Kan Al’ummar Jihar Jigawa
Published: 26th, February 2025 GMT
Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa ta bukaci hadin kan al’ummar jihar domin samun nasarar ayyukan da ta sanya a gaba.
Shugaban Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) Barista Salisu Abdu ya bayyana a matsayin wani muhimmin mataki na ci gaba da kokarin tabbatar da gaskiya da rikon amana a bangaren gwamnati.
Ya furta haka ne a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa ta shirya a cibiyar bunkasa ma’aikata dake Dutse.
Ya jaddada cewa, gaskiya, da rikon amana, su ne ginshikin gudanar da shugabanci nagari.
Barista Salisu Abdu, ya kuma yi kira da a hada kai tsakanin Hukumar da hukumomin gwamnati domin yakar cin hanci da rashawa yadda ya kamata.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, taron ya hada manyan masu ruwa da tsaki, da suka hada da wakilai daga ma’aikatar shari’a, shari’a, da ICPC, da EFCC, da PCC, inda aka mayar da hankali wajen ilmantar da mahalarta taron game da aikin hukumar, da tsarin shari’a, da kuma bangarorin hadin gwiwa.
Tattaunawar ta ta’allaka ne kan ingantattun ayyuka, da hanyoyin hana almundahana da ayyukan rashawa.
Taron bitar wanda ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ma’aikatan gwamnati, da masu ruwa da tsaki, ya yi nuni da yadda gwamnati mai ci ke kokarin inganta shugabanci nagari da kawar da cin hanci da rashawa domin share fagen samun ci gaba mai ma’ana a jihar.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cin Hanci Da Rashawa Jigawa da rashawa ta
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar Babura Sun Karrama Sabon Shugaban Asibitin Koyarwa Na Rasheed Shekoni
Al’ummar Babura sun shirya gagarumin taron girmamawa domin karrama Dr. Salisu Mu’azu, bayan nada shi a matsayin Daraktan kuma babban likitan asibitin koyarwa na Rasheed Shekoni da ke jihar Jigawa, da kuma samun matsayin mamba na Cibiyar Kasa (mni).
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kwamitin Shirye-shirye, Rabiu Umar, ya bayyana cewa an gudanar da taron ne domin nuna godiya ga Allah da kuma murnar manyan nasarorin da Dr. Mu’azu ya samu.
Ya yaba da kokarin Daraktan wajen gudanar da aikinsa da kwarewa, da kuma ci gaba da tallafa wa al’umma.
A sakon da aka gabatar a madadin Mai Martaba Sarkin Ringim, Alhaji Dr. Sayyadi Abubakar Mahmoud, wanda Mai Girma Alhaji Usman Sayyadi, Babban Hakimin Masarautar, ya wakilta, ya nuna godiya ga masu shirya taron.
Ya bayyana karramawar a matsayin abin da ya dace da Dr. Mu’azu, yana mai jaddada jajircewarsa, da tausayi da himma wajen yi wa al’umma hidima.
Haka zalika, Shugaban Karamar Hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu, ya taya Dr. Mu’azu murna bisa nasarorin da ya samu a fannin aikin likitanci, inda ya danganta hakan da jajircewa da amana.
Ya tabbatar masa da cikakken goyon bayan al’umma tare da addu’ar samun karin nasarori.
A nasa bangaren, Dr. Salisu Mu’azu ya bayyana godiya sosai bisa girmamawa da karramawar da al’ummarsa ta masa.
Ya kuma nuna godiya ga Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, bisa damar da ya ba shi zuwa makarantar NIPSS da ke jihar Filato.
A yayin taron, mutane da kungiyoyi daban-daban sun mika kyaututtuka da lambobin yabo ga Daraktan, ciki har da reshen kungiyar likitoci ta Najeriya na jihar Jigawa, J Health Beneficiaries, kungiyar Nas nas da Ungozoma ta kasa, da kuma kungiyar masu kula da lafiyar hakora ta Babura da sauransu.
Usman Muhammad Zaria