Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Nemi Hadin Kan Al’ummar Jihar Jigawa
Published: 26th, February 2025 GMT
Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa ta bukaci hadin kan al’ummar jihar domin samun nasarar ayyukan da ta sanya a gaba.
Shugaban Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) Barista Salisu Abdu ya bayyana a matsayin wani muhimmin mataki na ci gaba da kokarin tabbatar da gaskiya da rikon amana a bangaren gwamnati.
Ya furta haka ne a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Jigawa ta shirya a cibiyar bunkasa ma’aikata dake Dutse.
Ya jaddada cewa, gaskiya, da rikon amana, su ne ginshikin gudanar da shugabanci nagari.
Barista Salisu Abdu, ya kuma yi kira da a hada kai tsakanin Hukumar da hukumomin gwamnati domin yakar cin hanci da rashawa yadda ya kamata.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, taron ya hada manyan masu ruwa da tsaki, da suka hada da wakilai daga ma’aikatar shari’a, shari’a, da ICPC, da EFCC, da PCC, inda aka mayar da hankali wajen ilmantar da mahalarta taron game da aikin hukumar, da tsarin shari’a, da kuma bangarorin hadin gwiwa.
Tattaunawar ta ta’allaka ne kan ingantattun ayyuka, da hanyoyin hana almundahana da ayyukan rashawa.
Taron bitar wanda ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ma’aikatan gwamnati, da masu ruwa da tsaki, ya yi nuni da yadda gwamnati mai ci ke kokarin inganta shugabanci nagari da kawar da cin hanci da rashawa domin share fagen samun ci gaba mai ma’ana a jihar.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Cin Hanci Da Rashawa Jigawa da rashawa ta
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Litinin, 31 ga watan Maris, da Talata, 1 ga watan Afrilu, a matsayin ranakun hutun ƙaramar salla.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da sakataren ma’aikatar, Magdalene Ajani, ya fitar a ranar Laraba.
Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasuYa taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da yin kira a gare su da su ci gaba da halaye nagari da suka koya a watan.
Haka kuma ya jaddada muhimmancin soyayya, yafiya, da haɗin kai wajen gina al’umma.
Tunji-Ojo, ya buƙaci ’yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a domin samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, da ci gaban ƙasa.
Ya yi fatan cewa bukukuwan salla za su ƙara haɗin kai tsakanin mutane duk da bambancin addini da ƙabilanci da ake da su.
Haka kuma, ya yi kira ga jama’a da su yi bukukuwan ta hanyar tunawa da mabuƙata, ta yadda za a taimake su.
A madadin Gwamnatin Tarayya, ministan ya aike da saƙon fatan alheri ga dukkanin Musulmi tare da addu’ar Allah Ya sanya farin ciki a zukatan kowa.