Aminiya:
2025-03-28@18:45:23 GMT

Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan

Published: 26th, February 2025 GMT

Shugaban Kungiyar ’Yan Kasuwa Masu Hada-hadar Kayan Marmari a Jihar Oyo, Walin Ibadan, Alhaji Dauda Shehu ya ce, kungiyar za ta rage farashin kayan marmari domin samun sauƙi ga al’ummar Musulmi a cikin watan Azumin Ramadan.

Ya ce, “kamar yadda muka saba yi a baya a irin wannan lokaci, a bana ma za mu rage farashin kayan marmari kamar dankalin Turawa da karas da kukumba da latas da koren tattasai da ake fataucin su daga wasu jihohin Arewa zuwa Kudancin kasa.

Ahmed Musa ya buƙaci a gudanar da bincike kan mutuwar ɗan wasan Nijeriya a Uganda Mayaƙan Boko Haram sun sace kwale-kwale 8 a Borno

“Za mu yi ragin ne daidai gwargwado daga cikin ribar da muke samu saboda albarkar wannan wata’’, inji shi.

Da yake zagayawa da Aminiya sassa daban-daban na kasuwar kayan marmari ta Benjamin da ke Eleyele a Ibadan babban birnin Jihar Oyo, Alhaji Dauda Shehu ya ce, mun yi wata ganawa ta musamman a tsakaninmu da ’yan kasuwa masu fataucin irin wannan kaya daga jihohin Filato da Kaduna da Kano da Sakkwato.

Ya ce sun amince da yi wa kansu da al’ummar Musulmi adalci wajen sauko da farashin kayan a cikin kwana 30 na watan Azumin Ramadan, domin saukaka wa Musulmi da rage masu radadin tsadar rayuwa a wannan lokaci.

Sai dai ya ce, farashin wadannan kaya za su koma yadda ake sayar da su a baya da zarar watan Azumin ya kare.

Ya ce, “mun yi hakan ne saboda albarkar wannan wata na Ramadan, amma bayan kammala kwana 30 na watan Azumin, ya zama wajibi mu mayar da farashin wannan kaya kamar yadda muke sayarwa a baya domin ci gaba da rage farashin zai iya janyo mana asara.

“Muna daukar matakin rage farashin kayan ne bayan mun rage ribar da ke shiga aljihunmu.

Da yake amsa wata tambaya, Alhaji Dauda Shehu ya ce, “masu sarin irin wannan kaya daga sashen Kudu maso Yamma da suke rububin shigowa cikin wannan kasuwa ta Ibadan a kowane garin Allah Ya waye, mun ba su shawarar daukar matakin rage farashin kayan a garuruwan da suka fito, domin samun sauki ga Musulmi a cikin wannan lokaci.

Ya ce, “tashin farashin irin wannan kaya ba laifin mu ba ne, domin yanayi ne da ya shafi kasa baki daya da ke matukar bukatar ci gaba da addu’o’in rokon Allah samun sauki.”

Alhaji Dauda Shehu ya ce, a yanzu haka ana sauke nau’in irin wannan kaya a cikin manyan motoci uku zuwa biyar a kullum a cikin kasuwar ta Benjamin, inda manya da kananan ’yan kasuwa suke rububin saye domin baje-kolinsu a cikin shagunan cikin gari da masu yawon talla a kan hanyoyin birnin na Ibadan.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Oyo Kayan Marmari Watan Ramadan Alhaji Dauda Shehu ya ce rage farashin kayan irin wannan kaya kayan marmari watan Azumin

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan ta’adda Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Uku A Borno

Hakan ya sa, rundunar FOB ta yi kira da akawo musu dauki ta sama baya ga aikewa da karin tawaga ta kasa domin tallafawa. Duk da haka, tawagar ta sake cin karo da Bam a kan hanya.

 

Duk da cewa, ba a samu cikakken bayanin harin ba a lokacin rubuta wannan rahoton, amma an samu cewa, matukin jirgin yakin da aka aika domin bayar da agaji ta sama, ya sanar da cewa, yana iya hango wuta tana ta shi a kusa da FOB sannan wasu sojoji da dama na gudu zuwa Sabon Gari, kamar dai, an riga an kwace sansanin FOB din.”

 

Darakta, Ayyukan Yada Labarai na Tsaro, Manjo Janar Markus Kangye, bai amsa sakon da Wakilinmu ya aika masa ba domin tabbatarwa a lokacin fitar da wannan rahoton.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
  • Sallah: Yadda ake shirin caɓa ado duk da tsadar kaya
  • Majalisa ta buƙaci a rage kuɗin data don sauƙaƙa wa ’yan Najeriya 
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • Jagoran Juyin Musulunci Ya Amince Da Yin Afuwa Ga Wasu Fursunoni Masu Yawa
  • JIBWIS Ta Raba Kayan Abinci Na Kimanin Naira Miliyan 9 Ga Marayu
  • Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji
  • DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah
  • ‘Yan ta’adda Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Uku A Borno