Isra’ila Ta Kai Hare-hare A Kudancin Syria
Published: 26th, February 2025 GMT
Jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare da dama a kan wasu sansanonin soji a kudancin kasar Siriya, ciki har da wasu yankunan da ke wajen Damascus babban birnin kasar da kuma lardin Deraa da ke kudancin kasar.
Hare-haren dai ya biyo bayan kiran da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya yi na karbe yankin kudancin Siriya baki daya.
Jaridar Yedioth Ahronoth ta Isra’ila ta kuma bayar da rahoton cewa, Tel Aviv ta fara aiwatar da wani shiri na “shiga kudancin Syria.
Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya ce jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare a kudancin Syria a daren Talata, yana mai cewa harin wani bangare ne na sabuwar manufar Isra’ila ta “kawar da ayyukan soji a kudancin Syria.”
A cikin wata sanarwa da Katz ya fitar, ya ce harin wani bangare ne na manufar da firaminista Benjamin Netanyahu ya sanar a ranar Litinin, na “kawar da ayyukan soji kudancin Syria.”
Ya kara da cewa, za a tarwatsa duk wani yunkuri na dakarun sabuwar gwamnatin Syria da kungiyoyin ‘yan tawaye na kafa kansu a kudancin Syria.
A daya bangaren kuma, kafofin yada labaran kasar Syria sun rawaito cewa jiragen yakin Isra’ila sun kai hare-hare da dama a kudancin kasar ta Syria, yayin da sojojin kasa suka kutsa kai tsakanin Daraa da Quneitra dake kudancin kasar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a kudancin Syria kudancin kasar kai hare hare
এছাড়াও পড়ুন:
Ranar Kudus: al’ummar Iran zasu nuna hadin kan su ga duniya_ Pezeshkian
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi kira ga al’ummar kasar da su nuna hadin kai a yayin bukukuwan ranar Kudus ta duniya wato ranar JUma’ar kashe ta watan Ramadana da ke gabatowa, yana mai jaddada cewa hakan zai nuna matukar goyon bayan Jamhuriyar Musulunci ta Iran ga al’ummar Falastinu.
Pezeshkian, ya bayyana hakan ne a yayin taron majalisar ministocin kasar na farko sabuwar shekarar kalandar farisa, inda yake cewa “Ina fatan tare da halartar al’ummar kasar, za a gudanar da ranar Kudus mai daraja, kuma a wannan rana al’umma za su nuna hadin kai ga duniya.”
Ranar Kudus ta duniya dai marigayi Imam Khumaini ne ya ayyana ta kuma ana gudanar da ita a kowace shekara a ranar Juma’ar karshe ta azumin watan Ramadan domin nuna goyan baya ga al’ummar falasdinu.
Ta kasance wani gangami na duniya ga musulmi da masu neman ‘yanci a wajen bayyana goyon bayansu ga al’ummar Falastinu tare da yin Allah wadai da mamayar da gwamnatin Isra’ila ke yi wa yankunan Falastinawa da kuma cin zarafin da take yi wa masallacin Kudus.