Aminiya:
2025-02-26@21:03:48 GMT

Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N825 a Legas

Published: 26th, February 2025 GMT

Matatar Dangote ta rage farashin man fetur zuwa Naira 825 kan kowace lita a Jihar Legas.

Yanzu haka dai an samu ragin Naira 65, daga farashin da ake siyarwa a kan Naira 890 a baya.

Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Sabon farashin zai fara aiki daga ranar 27 ga watan Fabrairun 2025.

Matatar ta ce wannan matakin na nufin rage wa ‘yan Najeriya wahalhalun da suke fuskanta, yayin da azumin watan Ramadan ke ƙaratowa, tare da tallafa wa manufofin tattalin arziƙi na Shugaba Bola Tinubu.

“Rage farashin man fetur wani ɓangare ne na ƙokarinmu na sauƙaƙa wa ‘yan Najeriya,” in ji matatar Dangote.

“Za mu ci gaba da tabbatar da wadatar man fetur a farashi mai sauƙi.”

Wannan ragi, na nufin za a sayar da man fetur a gidajen mai a Legas kan Naira 860 kan kowace lita, Naira 870 a Kudu maso Yamma, da Naira 880 a Arewacin Najeriya.

A gidajen mai na AP da Heyden, farashin zai kasance Naira 865 a Legas, sai Naira 875 a Kudu maso Yamma, da Naira 885 a Arewacin Najeriya.

“Muna kira ga ‘yan kasuwa su mara mana baya don tabbatar da cewa ‘yan Najeriya sun ci gajiyar wannan sauƙi,” in ji matatar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya Matatar Dangote Rage Farashi Ramadan Tattalin Arziƙi

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu ‘Yan China 16 Da Ake Zargi Da Aikata Zamba Ta Yanar Gizo A Legas

An gurfanar da wadanda ake zargin ne bisa laifuka daban-daban, da ke da alaka da laifukan zamba ta yanar gizo, mallakar wasu takardu da ke dauke da shaidar karya, da kuma satar bayanan sirri.

 

Dukkansu sun ki amsa laifin da ake tuhumar su da su a lokacin da aka karanta musu tuhumar, sai dai lauyan masu shigar da kara, Nnaemeka Omewa, ya bukaci kotun da ta dage zaman shari’ar tare da tsare wadanda ake kara a gidan gyaran hali.

 

Mai shari’a Osiagor ya dage sauraron karar zuwa ranar 23 ga watan Yunin 2025 domin ci gaba da shari’a, sannan ya bayar da umarnin a tsare su a gidan gyaran hali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ɗangote Ya Rage Farashin Man Fetur Saboda Gabatowar Azumi
  • Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas
  • Gwamnatin Katsina Ta Ƙaddamar Da Shirin Tallafin Abinci Na Naira Biliyan 4
  • Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan
  • Babu hannun Naira Marley a mutuwar Mohbad — Kotu
  • EFCC Ta Gurfanar Da Wasu ‘Yan China 16 Da Ake Zargi Da Aikata Zamba Ta Yanar Gizo A Legas
  • NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi?
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Aikin Gyaran Titin Birnin Kudu Akan Kudi Naira Biliyan 11.5
  • NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri