Aminiya:
2025-02-27@00:17:30 GMT

Ukraine ta cimma yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai

Published: 27th, February 2025 GMT

Ukraine ta amince da wata yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai da cinikayyar albarkatun ƙasa.

Ana sa ran sanar da yarjejeniyar a hukumance a yau Laraba, inda za a ba wa kamfanonin Amurka dama su shiga harkar haƙar ma’adinai a Ukraine, ciki har da man fetur da iskar gas.

Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Bisa ga bayanai, Amurka za ta samu wani kaso mai yawa daga ribar da za a samu, wanda zai iya kai wa Dala biliyan 500.

Duk da cewa ba a bayyana batun tallafin tsaro a cikin yarjejeniyar ba, ministar shari’ar Ukraine, Olha Stefanishyna, ta ce akwai wasu muhimman batutuwa da Ukraine za ta amfana da su.

A ranar Juma’a mai zuwa ne shugaba Volodymyr Zelenskyy, zai tafi Amurka don ganawa da shugaba Donald Trump domin kammala yarjejeniyar.

Ukraine za ta riƙa saka kaso 50 na ribar da ta ke samu daga ma’adinanta a wata gidauniya ta haɗin gwiwa da Amurka, kuma wani ɓangare na kuɗin za a yi amfani da shi wajen sake gina ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ukraine yarjejeniya

এছাড়াও পড়ুন:

An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta

An cimma matsaya tsakanin Isra’ila da Hamas kan sakin fursunomin Falasdianwan nan 206 da Isra’ila ta jinkira, bayan da Hamas ta saki ‘yan Isra’ila shida.

An dai tsara sakin fursunonin a ranar Asabar data gabata, saidai Isra’ila ta jinkirta sakin falasdinawan bisa abinda ta kira rashin gamsuwa da cin wulakanta ‘yan kasarta gabanin sakin da kungiyar Hamas ke yi.

Bayanai sun ce za’a saki falasdinawan su 206 a cikin sa’o’I 24 masu zuwa.

Dangane da dakatar da sakin fursunonin, Hamas ta zargi Isra’ila da “saka dukkan yarjejeniyar tsagaita wuta a cikin hatsari mai tsanani” tare da yin kira ga kasashe masu shiga tsakani da su shiga tsakani.

A nata bangaren, Hamas za ta mika wasu gawawwakin ‘yan Isra’ila hudu da ta yi garkuwa da su.

Kuma za a yi hakan ne ba tare da wani biki ba, ba tare da shirya taron da kungiyar Hamas ta saba yi ba wajen sallamar wadanda ta yi garkuwa dasu.

Za a mika gawarwakin ne tare da kungiyar agaji ta Red Cross, amma kuma da taimakon Masar.

A cewar sojojin Isra’ila, daga cikin mutane 251 da aka yi garkuwa da su a ranar 7 ga Oktoba, 62 suka rage a Gaza, sannan 35 daga cikinsu sun mutu.

A ranar 1 ga watan Maris mai shirin kamawa ne ya kamata matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar ta tsakanin Isra’ila da Hamas ta kawo karshe, domin shiga mataki na biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Tace An Cimma Matsaya Da HKI Bayan Tsekon Da Aka Samu Na Sakin Fursinoni Falasdinawa 620
  • Wakilin Sin: Dole Ne A Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba
  • An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
  • Ministar Wajen Madagascar: Muna Godiya Ga Tawagogin Likitanci Na Sin
  • Tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.84 — NBS
  • MDD : Kwamitin Sulhu ya amince da kudurin Amurka kan rikicin Rasha da Ukrain
  • Rasha : Putin Ya Ce Turawa ‘Na Iya Shiga’ A Sasanta Rikicin Ukraine
  • Kasar Sin Ta Cimma Burin Magance Gurbatar Yanayi A Shekara Ta 2024