Aminiya:
2025-03-29@08:23:41 GMT

Ukraine ta cimma yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai

Published: 27th, February 2025 GMT

Ukraine ta amince da wata yarjejeniya da Amurka kan haƙar ma’adinai da cinikayyar albarkatun ƙasa.

Ana sa ran sanar da yarjejeniyar a hukumance a yau Laraba, inda za a ba wa kamfanonin Amurka dama su shiga harkar haƙar ma’adinai a Ukraine, ciki har da man fetur da iskar gas.

Dangote ya rage farashin man fetur zuwa N860 a Legas Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno

Bisa ga bayanai, Amurka za ta samu wani kaso mai yawa daga ribar da za a samu, wanda zai iya kai wa Dala biliyan 500.

Duk da cewa ba a bayyana batun tallafin tsaro a cikin yarjejeniyar ba, ministar shari’ar Ukraine, Olha Stefanishyna, ta ce akwai wasu muhimman batutuwa da Ukraine za ta amfana da su.

A ranar Juma’a mai zuwa ne shugaba Volodymyr Zelenskyy, zai tafi Amurka don ganawa da shugaba Donald Trump domin kammala yarjejeniyar.

Ukraine za ta riƙa saka kaso 50 na ribar da ta ke samu daga ma’adinanta a wata gidauniya ta haɗin gwiwa da Amurka, kuma wani ɓangare na kuɗin za a yi amfani da shi wajen sake gina ƙasar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ukraine yarjejeniya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce kasar Amurka ta yi amfani da batun kayayyakin da ake fitarwa zuwa kasashen waje, kamar jerin sunayen kamfanoni, wajen sanyawa sauran sassa takunkumai bisa hujjar “barazana ga tsaron kasa, da kuma keta manufofin diplomassiyar Amurka”, wanda hakan ya zama wani babban mataki na nuna fin karfi.

Guo ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci taron manema labarai na yau da kullum na yau Laraba, lokacin da yake tsokaci game da matakin Amurka na shigar da kamfanonin Sin fiye da goma, cikin jerin sunayen wadanda ta hana su shigar da hajoji Amurka, bisa jadawalin da ma’aikatar kasuwancin Amurka ta fitar. Game da hakan, Guo ya ce bangaren Sin zai dauki matakai don kiyaye hakki da muradun kamfanonin kasar Sin.

Kwalara Ta Kashe Mutum 14, Ana Zargin 886 Sun Kamu A Nijeriya – NCDC ‘Yan ta’adda Sun Kai Hari Sansanin Sojoji, Sun Kashe Uku A Borno

Dangane da rahoton da Amurka ta fitar game da “ka’idar barazana ta kasar Sin”, Guo Jiakun ya ce, Sin na shawartar Amurka da ta daina kallon dangantakar da ke tsakanin Sin da Amurka da tsohon tunanin yakin cacar baka, ta kuma daina yada kalaman nan na “barazanar kasar Sin”.

Game da tattalin arzikin Asiya kuwa, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin za ta sa kaimi ga samun ci gaba mai inganci, da bude kofa ga kasashen waje, da yin hadin gwiwa da sauran kasashen Asiya, wajen ba da sabbin gundumawa, don inganta ci gaban tattalin arzikin duniya. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abubuwan Da Za Su Iya Kawo Cikas Ga Bukukuwan karamar Sallah
  • Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno
  • A Cikin Mako Daya An Yi Asarar Naira Biliyan 365 A Kasuwar Sayar Da Hannun Jari
  • Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m
  • Iran Ta Bada Amsa Ga Wasikar Shugaban Kasar Amurka Ta Gayyatar Kasar Zuwa Tattaunawa Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana
  • Miliyoyin  ‘Yahudawa Sun Gudu Neman Mafaka Saboda Makamin Mai Linzami Daga Yemen
  • Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta
  • Kamfanonin Sin Za Su Samar Da Hidimomin Kyautata Amfani Da Makamashi Mai Tsafta A Afirka Ta Kudu
  • Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano