Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Saad Abubakar ya yi kira ga al’ummar Musulmin kasar nan da su fara neman ganin jinjirin watan RAMADAN a gobe Juma’a 28 ga watan Fabrairu 2025, daidai da kalandar Musulunci 29 ga watan Sha’aban1446AH.

 

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun shugaban kwamitin ba da shawara kan harkokin addinin musulunci na jihar Sokoto, Farfesa Sambo Wali Junaidu, Wazirin Sokoto ya ce idan an gan shi, sai a mika bayanan ga Dagaci, Hakimi, Mai Unguwa ko Sarki mafi kusa domin sanarda Mai Alfarma Sarkin Musulmi.

 

Sanarwar ta ci gaba da cewa, duban wata, yana fayyace kalandar Musulunci a cikin shekara guda, wanda hakan ya sa ganin watan Ramadan ya fi karbuwa ga daukacin Musulmin kasar.

 

Za iya amfani da lambobin nan kai tsaye don sanarda Mai Alfarna Sarkin Musulmi labarin ganin wata

 

08037157100, 08066303077, 08035965322, 08099945903, 07067146900

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Duban Fari Ramadan Wata Sarkin Musulmi

এছাড়াও পড়ুন:

Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin

A yau Juma’a aka kammala taron shekara-shekara na dandalin tattaunawa na kasashen Asiya na Boao. Cikin kwanaki 4, kimanin wakilai 2,000 daga kasashe da yankuna sama da 60 ne suka hallara a lardin Hainan na kasar Sin tare da musayar ra’ayi mai zurfi karkashin jigon na “Gina makomar asiya a duniya mai sauyawa.”

A matsayinta na mai masaukin bakin, kasar Sin ta gabatar da shawarwari 4 da suka yi daidai da ra’ayin mahalarta taron. Shawarwarin sun hada da karfafa hadin kai da hadin gwiwa wajen inganta aminci, da inganta dunkulewar tattalin arzikin duniya ta hanyar bude kofa da dunkulewa, da samar da ci gaba da wadata na moriyar juna, da kiyaye zaman lafiya da tsaro da zaman jituwa.

Alkaluma sun nuna cewa, a shekarar 2024, an kafa kusan sabbin kamfanoni 60,000 masu jarin waje a kasar Sin, adadin da ya karu kan na 2023 da kaso 9.9. Haka kuma, cikin shekaru 5 da suka gabata, ribar jarin kai tsaye da aka zuba a kasar Sin ta kai kimanin kaso 9, inda adadin ya shiga cikin wadanda ke kan gaba a duniya. A yayin da ake fama da rashin tabbas a duniya, kasar Sin na kara fadada bude kofarta da ingiza kwanciyar hankali a duniya mai hargitsi. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gobe Ta Ke Sallah A Nijeriya – Sarkin Musulmi
  • Gobe take Sallah a Nijeriya
  • Gobe take Sallah a Nijeriya — Sarkin Musulmi
  • Saudiyya ta sanar da hango watan Shawwal, ranar lahadi ce Sallah a kasar
  • An Tabbatar Da Ganin Watan Shawwal A Nijeriya
  • An Ga Watan Sallah A Ƙasar Saudiyya
  • An ga watan Sallah a Saudiyya
  • JIBWIS Giwa Ya Bukaci Al’ummar Yakawada su Rike Darussan Al-Qur’ani
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • A fara duban watan Shawwal – Sarkin Musulmi