Shin Kwankwasiyya ta kama hanyar wargajewa ne?
Published: 28th, February 2025 GMT
A ranar Litinin ne Jam’iyyar NNPP ɓangaren Kwankwasiyya a Kano, ta fitar da sanarwar dakatar da jiga-jigan ’yan siyasarta huɗu.
An dakatar da Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila, da sauran ’yan majalisar wakilai uku, da suka haɗa da Aliyu Sani Madakin Gini da Kabiru Alhassan Rurum da kuma Abdullahi Sani Rogo.
Sai dai ba kowa ne ya san asalin mafarin rigimar ’yan majalisar da madugunnKwankwasiyyam Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ba.
Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli.
Yadda kasuwar buƙata ta haɗe su da Kwankwaso a 2023
Dama dai ana ganin Sani Rogo da Kawu Sumaila, asali ba su da gami da tafiyar siyasar Kwankwasiyya, amma saboda kasuwar buƙata ce, suka haɗe daga baya.
Abdullahi Sani Dogo ya koma jikin Kwankwaso ne tun bayan raba gari da tafiyar gidan Malam Ibrahim Shekarau.
Shi kuma Kawu Sumaila, ya koma jikin Kwankwaso ne gab da zaɓen 2023.
Kabiru Alasan Rurum, asali ɗan Kwankwasiyya ne, amma ya bart a a lokacin Gwamnatin Ganduje, har ya zama Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano. Sai dai bayan hana shi takarar gwamna a Jam’iyyar APC, ya koma gidansa na da, wato Kwankwasiyya.
Wanda aka fi yin mamakin saɓaninsa da tsarin Kwankwasiyya shi ne Ali Sani Madakin Gini, ganin yadda a zamanin Ganduje, ya rasa kujerar ɗan Majalisar Tarayya saboda nuna biyayya ga Kwankwaso.
Ainihin tushen saɓaninsu da Kwankwaso
Saɓanin ya faro ne a lokacin da Kwankwaso da kansa ya jagoranci fitar da shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli, ba tare da bai wa ɗaya da cikin waɗannan jiga-jigai dama ba.
Majiyoyi sun tabbatar da cewa, babu wanda aka bai wa dama a cikinsu a fitar da shugabancin ƙananan hukumomin da suka fito, abin da suke ganin tamkar cin fuska ne ga buwayarsu ta siyasa.
Misali da ƙaramar hukumar Sumaila, a yadda aka saba, Kawu Sumaila shi yake kafa shugabanci a matakin ƙaramar hukumar, amma a wannan karon, Kwankwaso ya bai wa Faruk Abdu, ɗan tafiyarsa na asali, wanda kuma bai cika shiri da Kawu Sumaila ba a siyasance.
Tun daga lokacin ake zaman doya da manja, har ake zargin ’yan majalisar da ƙara rura wuta a tafiyar Abba Tsaya da Kafarka da ta kunno kai a kwanakin baya.
Makomar siyasar Kwankwasiyya
A yanzu haka, ’yan majalisar da aka dakatar sun barranta kansu da NNPP mai littafi, inda suka bayyana cewa, su ’yan Jam’iyyar NNPP mai kayan marmari ne. Kuma a yanzu haka maganar tana kotu, kan wane ɓangare ne ke da halaccin a matsayin jam’iyya.
’Yan Kwankwasiyya a Kano na kallon ’yan majalisar huɗu a matsayin masu butulci. Misali da Kawu Sumaila da ya daɗe yana neman Sanata bai samu ba, har sai da ya haɗa tafiya tare da Kwankwaso.
Ana ganin Kwankwasiyya ka iya samun rauni, musamman a Kano ta Kudu, idan har aka tafi a haka. Kuma da ma tun a zaɓen 2023, Kwankwasiyya ba ta da ƙarfin a-zo-a-gani a yankin Kano ta Arewa.
Abun jira a gani shi ne ko Kwankwaso zai yafe wa ’yan majalisar, a tunkari zaɓen 2027 tare, tun da dai siyasa kasuwar buƙata ce.
Ko kuma zai zaɓi zama shi ƙadai gayya a zaɓe mai zuwa, kamar yadda ya sha gwadawa a baya tana kai masa.
Idan ko hakan ya zaɓa, tabbas za a doka siyasa, kuma a cikin biyu a yi ɗaya: Walau ya koya musu darasinta, ko kuma su nuna masa ƙarfinsu ya kawo.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kawu Sumaila Kwankwasiyya Kwankwaso Siyasa yan majalisar Kawu Sumaila da Kwankwaso
এছাড়াও পড়ুন:
Masu garkuwa za su mutu ta hanyar rataya a Edo – Okepebolo
Gwamnan Jihar Edo, Monday Okpebholo ya bayyana cewa masu garkuwa da mutane da aka samu da laifi a jihar za su fuskanci hukuncin kisa ta hanyar rataya.
Okpebholo ya bada tabbacin a shirye yake ya sanya hannu akan sammacin kisa na waɗanda aka yankewa hukunci a jihar idan kotu ta same su da laifi.
An tsinci gawar mabaraci mai shekara 75 a Neja PDP ba ta shirya yin zaɓen 2027 ba – WikeGwamna Okpebholo ya bayyana hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a garin Uromi, inda ya tattauna da shugabanni da ’yan uwa na yankin unguwar ’yan Arewa mazauna Esan.
“Ku tuna cewa Majalisar Dokokin Jihar Edo (EDHA) ta zartar da wani ƙudiri na gyara dokar hana garkuwa da mutane (da wasu dokoki da suke da alaƙa da na shekarar 2013)”.
Ƙudirin dokar ya tanadi hukuncin kisa ga masu garkuwa da mutane sannan kuma ya ba da umarnin ƙwacewa da rushe dukiyoyin da ake yin amfani da su wajen aikata laifukan.
A cewar gwamnan, gwamnatinsa ba za ta lamunci rashin tsaro, kisan gilla da kuma garkuwa da mutane ba.
“Na ɗauki batun rashin tsaro da muhimmanci kuma ba zan karkatar da ƙa’idar ba sai dai a yi amfani da su sosai, sabuwar dokar jihar ta ba mu damar rusa kadarorinsu da ƙwace musu filayensu.
“Za mu kawo masu garkuwa da mutane a gaban jama’a, mu kashe su domin mu nuna muhimmancinmu a kan dokokin da Majalisar Edo ta riga ta yi, ba zan ji tsoron sanya hannu a kai ba,” in ji shi.
Gwamnan ya yi kira ga kowa da kowa da su ba gwamnatinsa haɗin kai don tabbatar da tsaron jihar, yana mai cewa “tsaro aikin kowa ne ba na hukumomin tsaro kaɗai ba”.