Abubuwan Da Suka Ta Da Kura A Litttafin Janar Babangida
Published: 28th, February 2025 GMT
Har ila yau, a cewarsa; Abiola ya samu mafi yawan kuri’u tare da cika dukkanin sharudan da ake bukata, domin zama shugaban kasa. “Babu tantama a zuciyata, Abiola ne ya lashe wannan zabe tare da cika dukkanin sharudan da ake bukata”, in ji IBB.
Kazalika, ya kuma bayyana farin cikinsa; kan yadda Buhari ya karrama Abiola da lambar yabo mafi girma ta GCFR, wadda ake bai wa shugabannin kasa.
“Ko shakka babu, Mashood Abiola shi ne ya lashe zaben shugaban kasa a 1993, da kuri’u sama da miliyan takwas a jam’iyyasa ta SDP, inda ya samu nasara a kan abokin karawarsa, Alhaji Bashir Othman Tofa na jam’iyyar NRC”, in ji Babangida.
A jawabinsa na godiya, IBB ya bayyana rushe zaben 1993 a matsayin wani abu da ya yi yake kuma da-na-sanin yin sa a rayuwarsa.
Har ila yau, Janar Babangida a cikin littafin nasa, ya bayyana dalilinsa na kifar da gwamnatin Buhari, duk kuwa da cewa; shi ne babban hafsan sojin kasar a 1985.
Guda daga cikin dalilan nasa su ne, a babi na shida ya bayar da hujjar cewa; juyin mulkin, wani martani ne ga korafe-korafen ‘yan Nijeriya na bakar azaba da wahalar da suka sha da kuma tabarbarewar al’amuran kasar baki-daya.
“A farkon shekarar 1985, ‘yan Nijeriya sun fara fargaba game da makomar kasarmu, wanda al’amuran suka kasance a matsayin masu matukar hadari, wanda kuma hakan yanzu ma alamu ne a fili na irin wancan hatsari.
“Babu shakka, a bayyane yake ga shugabancin sojoji cewa, aikin da muka yi da nufin ceto kasarmu a shekarar 1983 ya tarwatshe”, kamar yadda ya rubuta a littafin.
Ya kara da cewa, rashin daukar mataki zai iya kawo rarrabuwar kawuna a tsakanin sojoji, wanda a ganinsa; hakan kan iya haifar da mummunar illa ga kasar.
“Idan sojoji suka samu rarrabuwar kai, al’ummar kasa za su bi sahunsu; sannan abin da zai biyo baya na iya kasancewa mai matukar ban tsoro da ba a taba tunani ba”, a cewarsa.
IBB, ya ci gaba da bayyana cewa, a shekarar 1983; sojoji sun hambarar da gwamnatin Shehu Shagari ne cikin hadin kai, amma sai aka fara samun rarrabuwar kawuna a tsakaninsu daga bisani.
“A matsayin sojoji na wadanda aka sani da hadin kai, sai ga shi kuma an fara samun guna-guni a tsakaninsu, wannan ne yasa dole a yi wani abu, don gudun kada mu rasa kasar”.
Babangida ya ce, “Babban abin da na ji tsoro shi ne, samun rarrabuwar kawuna da ra’ayoyi a tsakanin sojoji na iya haifar da bangaranci a tsakaninsu, wanda idan kuma aka bari abin ya ci gaba da samun gindin zama, akwai hatsarin gaske”.
Haka zalika, ya zargi Buhari da mataimakinsa Birgediya Janar Tunde Idiagbon da mayar da sojoji saniyar ware tare kuma da daukar tsauraran matakan kama-karya wajen tafiyar da mulki.
A cewar tasa, gwamnatin Buhari ta yi mulki ta hanyar tsoratarwa, maimakon sanya kyawawan fata a zukatan al’umma.
“Kyautuwa ya yi mu inganta rayuwarsu, mu karfafa musu gwiwa, don ganin rayuwar tasu ta inganta. Maimakon haka, sai aka yi ta faman kafa musu dokokin kama-karya. Wannan dalili ne yasa, aka wayi gari gwamnatin da aka kafa da niyyar cimma muradun bai-daya na sojoji, ta koma ta wasu ‘yan tsirarun mutane masu taurin kai”, in ji Babangida.
Ya bayyana cewa, “Yawancin juyin mulkin soja, muna yi ne sakamakon yawan korafe-korafen al’umma, musamman Talakawan da suka shiga matsanancin halin rayuwa, sakamakon tabarbarewar tattalin arziki da aka yi ta faman fuskanta na yau da kullum”.
“Haka zalika, batun komawa amfani da tsohuwar hanyar aiwatar da musayar kayayyaki a kasuwanci na kasa da kasa, na nufin cewa; kwata-kwata ba a kama hanyar kawo karshen matsalolin tattalin arzikin a tsakanin al’umma ba”, in ji IBB.
Har wa yau, sanin kowa ne cewa; dokokin kama-karya, sun tauye ‘yancin walwalar jama’a kai tsaye, sannan kuma ga hukunci mai tsauri, kamar yadda ya bayyana a littafin.
Kazalika, kayayyakin masarufi da sauran bukatun yau da kullum, sun yi matukar karanci, duk dai a wancan lokaci na mulki Buhari, in ji Babangida.
A bangare guda kuma, Janar Babangida a cikin littafin nasa, ya zargi marigayi tsohon shugaban kasa; Janar Sani Abacha da laifin yunkurin kifar da gwamnatinsa ta karfi da yaji da kuma zargin laifin soke zaben shugaban kasa na shekarar 1993.
Badamasi, ya amince da aikata babban kuskure a lokacin da yake shugabancin Najeriya, na gaza yi wa Sani Abacha ritaya daga aikin soja.
A lokacin, Abacha shi ne babban hasfan tsaro; wanda ya kwace mulki tsawon wata uku, bayan Babangida ya ajiye mukaminsa na shugabancin kasa.
Babangida ya kara da cewa, duk da shi da Abacha abokan juna ne, amma a fili yake cewa; Abacha mutum ne mai wuyar sha’ani, wanda ke biye wa munanan zantukan da ke faruwa a tsakanin rundunar sojin Nijeriya.
“Na yi mamakin yadda shi da wasu mutane suke da mummunar fahimta a kaina tare da nuna cewa, ni ne matsala,” in ji Babangida”.
A cikin littafin nasa ya ce, Abacha ne ya kitsa yadda za a cire shi daga shugaban kasa. Sai dai duk da haka, bai sallame shi daga aikin soja ba, saboda gudun zubar da jini a cikin rundunar sojin.
“A lokacin kan jami’an rundunar soji a rarrabe yake, don haka; duk wani yunkuri a lokacin, ka iya haifar da mummunar matsala,” in ji Babangida.
“Abin ya kai ga idan na yi wani kuskure daga bangarena, zai iya jawo zubar da jini, saboda za a samu yunkurin yin juyin mulki.”
Wannan tsokaci da IBB ya yi a littafin nasa, ya ja hankalin iyalan marigayi Sani Abacha, da ta kai har guda daga cikin ‘ya’yansa; Sadik Abacha ya mayar masa da martanin cewa, ‘yan Nijeriya ba za su taba mantawa da kokarin da mahaifinsu ya yi a bangaren ci gaban kasa ba, sannan kuma za su ci gaba da yaba masa kamar yadda suka saba.
“Mahaifina Abacha, kai ne a koda-yaushe suke yi maka hassada da bakin ciki. Saboda haka, tarihi zai ci gaba da tunawa da kai a matsayin shugaba nagari, ko su yabe ka; ko su yi suka, a matsayina na da, ina alfahari da kai, domin kuwa dukkaninsu suna fatan kai wa rabin matsayinka”, in ji Sadik.
Bugu da kari, makudan kudaden da aka tara a wajen kaddamar da littafin, ya yi matukar jawo cece-kuce a tsakanin ‘yan Nijeriya, domin kuwa Naira na gugar Naira har biliyan 17.5 aka tara wa tsohon shugaban kasar; don gina dakin karatu.
Har ila yau, Alhaji Aliko Dangote, Abdussamad Rabi’u, Janar TY Danjuma, Arthur Eze da sauran makamantansu, su ne wadanda suka tara wadannan makudan kudade; a matsayin gudunmawa, domin gina wannan katafaren dakin karatu na Janar Babangida.
Wanda ya fi kowa tarin dukiya a dukkanin fadin Afirka, Aliko Dangote, ya bayar da gudunmawar Naira biliyan biyu tare kuma da alkawarin ci gaba da bayar Naira biliyan biyu-biyu tsawon shekara uku, wanda idan aka hada jimillarsu zai kama Naira biliyan takwas.
Sai kuma Alhaji Abdussamad Rabi’u, wanda ya bayar da Naira biliyan biyar; duk da cewa, IBB ya bayyana cewa; tuni ya fara bayar da tasa gudunmawar wajen ginin wannan daki na karatu.
Akwai kuma, tsohon hafsan soji kuma ministan tsaro; TY Danjuma da ya yi alkawarin bayar da Naira biliyan uku. Sai wani shahararren Dan kasuwa mai suna Arthur Eze, shi ma ya bayar da gudunmawar Naira miliyan 500.
Haka nan, akwai wasu da dama su ma da suka bayar da wannan gudunmawa da kuma wadanda suka yi alkawari; duk dai a wajen wannan kaddamar da katafaren littafi na Janar Ibrahim Badamasi Babangida.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Kura Janar Babangida Naira biliyan yan Nijeriya ya bayar da
এছাড়াও পড়ুন:
Abubuwan Da Za Su Iya Kawo Cikas Ga Bukukuwan karamar Sallah
Tsadar rayuwa tun daga wancan lokacin ne bayan cire tallafin mai,da kwana daya kawai zuwa biyu sai rayuwar wasu dole ta fara sauyawa,kaya ko kayayyakin da ake saya a farashi na kashi 75 zuwa 100 sai abin ya koma farashin wasu har sai da,ya kai kashi 200 zuwa kashi 300 kai wani abin ma, har ya zarce haka,kuma kamar yadda Hausawa suka ce dole ce kanwar na ki ta sa hakan ta kasance,wannan kuma haka ne. Dole ce tasa haka saboda har an kai ga ganin abinda ya cirewa Buzu nadi wato wahala ke nan.Kuma dole ne cin kasuwa da makiyi wasu abubuwan abin ba,a iya cewa komai sai dai ayi gum da Baki kawai.
Matsalar tsaro
Ko shakka babu lamarin tavarvarewar tsaro ba karamin koma baya ya kawo ba na lamarin zamantakewa tsakanin al’umma abu tun daga wannan unguwa zuwa waccan har,ta kai ga daga wannan babban gari ma zuwa wancan har ta kai ga daga wannan Jiha zuwa waccan.Irin halin da al’umma suka tsinci kansu ke nan lamarin da ya kan yi tafiyar Kura yadda take gaba sai ta koma baya. Arewa ta sassa daban- daban tana fama da matsalar data shafi tsaro tunda kuwa ana yin garkuwa lokaci,anan matafiya wasu Jihohi na sashen Arewa maso yamma kamar Kaduna, Katsina,Zamfara,Sakkwato,da kuma Kebbi,masu ta shi daga Abuja zuwa gida wasu suna kan hanyar tasu ake tsaida su a kwashi mutane kamar Dabbobi ayi cikin daji dasu,kai har ma,ta kai ga mutane ko,a gidajensu suke basu tsira ba ana iya zuwa kowane lokaci ayi awon gaba dasu sai kuma yadda Allah yayi.Yayin da wasu suna dawowa wasu kuwa sun tafi ke nen sai dai aji labarin an kashe su,wasu ko ma an kai kudin fansar ba,za’a sake su ba.Irin hakan ce ta sa wasu yanzu basu zuwa gida Sallah saboda tsoron aukuwar irin hakan,maimakon hakan sai su yi hakuri su rungumi kaddara ta yin rayuwa kamar irin cikin halin,da suka samu kansu.
Tafiya zuwa yawon Sallah daga wannan unguwa zuwa waccan ko daga wannan gari zuwa wancan,halin da ake ciki yanzu hakan bata yiyuwa ba domin komai ba sai saboda tsoron irin abinda ka iya faruwa gare su,maganar gaskiya yanzu lamarin tsaro ya sa mutane da yawa sun,shiga cikin halin tsoro saboda komai yana iya faruwa a lokacin da ba ayi tsammanin hakan ba.Ba ance babu tsaron bane gaba daya amma su wadannan masu tayar,da zaune tsaye ko ina suna iya zuwa saboda ai suna da wadanda suke basu halin da ake ciki da su kan samu na su kason idan an yi sa’ar dauka da kuma garkuwa da mutane aka kuma biya kudin fansar.
Al’umma da dama basa garuruwan su na asali
Mutane da dama yanzu wasu ma ba Jihar su ta asali suke ba,wasu suna wata Jiha,kai akwai ‘yan Nijeriyar da har yanzu suna kasashen Nijar ko kuma Kamaru,idan ma sun yi sa’ar suna Jihar tasu ne,to su kan kasance ne a wani sansanin ‘yan gudun hijira ne wato wuraren da aka tsugunnar dasu,sanin kowa ne,babu yadda rayuwa za ta yi daidai ga wasu a,irin wadancan wuraren saboda can ma din da akwai nau’oin matsalolin da suke fuskanta a can.Ana iya tunawa shifa sansanin ‘yan gudun hijira wuri ne da aka ware na musamman wanda ake taimakawa nau’oin mutanen da suka fuskanci matsala babu yadda za su iya yi wajen tafiyar da rayuwarsu.Daga karshe sanin kowa ne duk wanda bai garin shi na asali rayuwa Lami yake yin ta domin a matukar takure yake.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp