Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-02-28@12:29:52 GMT

Kwara ta Raba Littafai Fiye da Dubu 74 Kyauta Ga Dalibai

Published: 28th, February 2025 GMT

Kwara ta Raba Littafai Fiye da Dubu 74 Kyauta Ga Dalibai

Sama da litattafai 73,000 na koyarwa da kayan wasanni, gwamnatin jihar Kwara ta raba wa daliban makarantun firamare da kananan sakandare a fadin jihar.

 

Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq da yake jawabi a wajen taron raba kayayyakin a Ilorin, ya ce sauran kayayyakin da za a raba sun hada da dakunan karatu na firamare 12,780; guda 100 na kayan ilimi na musamman; 260 na Kula da Yara da sauransu.

 

Gwamna AbdulRazaq wanda ya samu wakilcin kwamishiniyar ilimi da ci gaban jama’a ta jihar, Hajiya Sa’adatu Modibbo Kawu, ta ce  wannan wani shiri ne a cikin jerin shirye-shiryen da gwamnatin ke yi wanda ke nuni da fifikon da take da shi na samar da ilimin boko a jihar.

 

A cewarsa ra’ayin gwamnati ne cewa zuba jari zai mayar da matsalar yaran da ba su zuwa makaranta ya zama tarihi a jihar.

 

Gwamna AbdulRazaq ya bayyana cewa rabon litattafan kyauta shine don a rage musu nauyi a kan iyaye saboda tsadar kayan koyarwa a kasuwanni.

 

Ya ce gwamnatin ta kuma fara daukar malamai aiki akai-akai tare da kara musu girma idan sun cancanta, da kuma inganta abubuwan more rayuwa a makarantu da sauran hanyoyin da za a bi wajen kawo sauyi a fannin.

 

Gwamnan ya yabawa jami’an hukumar ta UBEC da sauran masu ruwa da tsaki bisa yadda suke ba da goyon baya da jajircewa wajen gudanar da aikin.

 

A nasa bangaren shugaban kwamitin majalisar dokokin jihar Kwara kan harkokin ilimi, Muhammed Boriya, ya bayyana taron a matsayin wani lokaci mai cike da tarihi na ci gaban ilimi na farko a jihar.

 

Ya ci gaba da cewa a yanzu jihar ta fice daga munanan abubuwan da suka faru a baya, inda ya ce an cike gibi da dama a bangarori da dama.

 

A nasa jawabin shugaban hukumar SUBEB ta jihar Kwara, Farfesa Shehu Adaramaja, ya ce raba kayan wasanni za su samar da ingantaccen ilimi da kuma bunkasa ci gaba ga yaran makaranta.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kayan Karatu Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi

Gidauniyar Sarki Salman ta Saudi Arabiya ta bayar da tallafin kayan abinci ga marasa ƙarfi 2,450 a Jihar Kebbi ta hannun hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA). An gudanar da rabon ne a Birnin Kebbi, inda aka raba buhuhunan shinkafa da wake mai nauyin kilo 25, garin masara kilo 2, da man gyada. An gudanar da rabon kayan ne a ɗakin ajiyar abinci na gwamnatin jihar da ke Bulasa.

Mataimakin Gwamnan Jihar Kebbi, Sanata Umar Abubakar Tafida, wanda ya wakilci Gwamna Nasir Idris a wajen rabon, ya gode wa gidauniyar bisa tallafin da ta ke bai wa mutanen jihar.

Amurka Da Rasha Sun Kammala Tattaunawar Kawo Ƙarshen Yakin Yukiren A Ƙasar Saudiyya Hajjin 2025: Kamfanin Saudiyya Ya Amince Da Kwangilar Aiki Da NAHCON Bayan Sabunta Yarjejeniya 

Ya ce wannan ba shi ne karo na farko da gidauniyar ke taimakawa ba, yana mai yabawa da kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin su da ƙasar Saudi Arabiya, musamman kan ayyukan jin ƙai da aikin hajji. Gwamnatin jihar ta yaba da rawar da NEMA ta ke takawa wajen rabon tallafin.

Shugabar hukumar NEMA ta ƙasa, Hajiya Zubaida Umar, wadda Hajiya Fatima Kasim ta wakilta, ta ce gidauniyar Sarki Salman ta dauki tsawon lokaci tana bayar da irin wannan tallafi tun daga shekarar 2018 domin taimakawa marasa galihu a Nijeriya. Ta bayyana cewa bayan Kebbi, za a ci gaba da rabon kayan abinci a jihar Adamawa. NEMA ta gode wa gwamnatin tarayya da Gwamnatin Jihar Kebbi bisa haɗin kan da suka bayar wajen ganin an aiwatar da aikin cikin nasara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kebbi Ta Kashe Naira miliyan 67 Wajen Biya Sadakin Ma’aurata 300
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Ce Har Yanzu Akwai Guraben Biyan Kujerar Hajji
  • Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje
  • Gwamnatin Kwara Ta Kaddamar Da Kwas Ga Dalibai Makarantun 50
  • Gwamna Sule Ya Hori Masu Ziyarar Ibada Ta Kirista Su Zama Jakadu Na Gari
  • Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi
  • Gwamna Namadi Ya Nada Jami’an Alhazai 27 Tare Da Kara Wa’adin Biyan Kudin Aikin Hajji
  • Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano
  • Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙa kayan makaranta a Kano