Aminiya:
2025-04-01@03:01:54 GMT

Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta

Published: 1st, March 2025 GMT

Azumin watan Ramadan na daga cikin shika-shikan Musulunci, kuma Allah ne Ya wajabta shi a kan bayinsa.

Wannan wata yana da falala da lada mai yawa, domin Allah Ya keɓe shi da girma da ɗaukaka.

Ga wasu daga cikin falalar azumin watan Ramadan:

1. Ana buɗe kofofin Aljanna, ana rufe ƙofofin wuta, kuma ana ɗaure shaiɗanu.

Wannan yana taimaka wa zuciyar Musulmi wajen yin alheri da kauce wa munanan ayyuka.

2. Yin azumi da tsayuwar sallar Tarawihi saboda Allah da neman lada, ana gafarta zunuban bawa da suka gabata.

3. Akwai daren Lailatul-Kadari, wanda ya fi wata dubu daraja. Duk wanda ya yi ibada a wannan dare yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa na baya.

4. Yin Umara a watan Ramadan yana daidai da yin aikin Hajji tare da Manzon Allah (SAW).

5. Watan Ramadan wata ne na Alƙur’ani, saboda a cikinsa aka saukar da shi. Don haka, ya dace a yawaita karanta shi.

6. Watan Ramadan wata ne na kyauta, ciyarwa da sadaka. Manzon Allah (SAW) ya fi yawan kyauta a wannan wata.

7. Baccin mai azumi ibada ne, domin yana rage sha’awa da kula da zuciya.

8. Mai azumi yana da farin ciki biyu:

Yayin da zai buɗe baki bayan azumi. Lokacin da zai haɗu da Allah (S.W.A.) ranar alƙiyama.

9. Azumi garkuwa ne daga wutar Jahannama. Yana kare mutum daga sharrin sha’awa da zunubi.

10. A Ramadan, Allah Yana ’yantar da bayinsa daga wuta. Duk wani dare, Allah Yana yafe wa bayinsa kuma yana kuɓutar da su daga azabar lahira.

Wannan wata mai albarka yana ƙarfafa imani, ibada, da kyautatawa.

Don haka, ya kamata Musulmi su yi amfani da watan Ramadan don samun kusanci ga Allah da aikata kyawawan ayyuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kyautatawa Manzon Allah SAW Ramadan watan Ramadan

এছাড়াও পড়ুন:

JIBWIS Giwa Ya Bukaci Al’ummar Yakawada su Rike Darussan Al-Qur’ani

Kungiyar JIBWIS a Karamar Hukumar Giwa ta bukaci al’ummar Yakawada da su ci gaba da rungumar koyarwar Al-Qur’ani a rayuwarsu ta yau da kullum.

Mataimakin Shugaban kungiyar, Malam Ibrahim Mustafa Shatiman Giwa, ya yi wannan kira ne yayin bikin rufe Tafsirin Ramadan na bana da aka gudanar a Masallacin JIBWIS da ke Yakawada.

Malam Ibrahim Mustafa ya bayyana jin daɗinsa kan goyon baya da jajircewar al’ummar Yakawada a duk tsawon Tafsirin. Ya jaddada muhimmancin kiyaye darussan da aka koya a cikin Ramadan tare da amfani da su a rayuwa bayan karewar watan mai alfarma.

A nasa jawabin, Sheikh Suleman Abdulkarim Fatika ya nuna godiyarsa ga dukkan mahalarta Tafsirin da suka daure suka halarta tun daga farkon watan Ramadan har zuwa karshensa.

Ya yaba da sadaukarwarsu tare da ƙarfafa su da su ci gaba da neman ilimi da fahimtar addini.

Taron rufe Tafsirin Ramadan din ya samu halartar malamai, shugabannin al’umma, da musulmi mabambanta, wanda hakan ya jaddada mahimmancin koyarwar addini wajen haɓaka haɗin kai da kyawawan ɗabi’u a cikin al’umma.

COV/Magaji Yakawada

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Azumin Sitta Shawwal a Musulunci
  • Iran Ta Ce Tattaunawa Da Amurka Tare Da Mai Shiga Tsakani Na Gaba, Ya Danganci Matakan Da Ta Dauka Kan Iran
  • Wani Asbiti A Amurka Ya Kori Wata Likita Daga Aiki Bayan Ta Yi Allawadai Da Yahudawan Sahyoniyya
  • Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina
  • Gobe Ta Ke Sallah A Nijeriya – Sarkin Musulmi
  • Gobe take Sallah a Nijeriya
  • Gobe take Sallah a Nijeriya — Sarkin Musulmi
  • An Tabbatar Da Ganin Watan Shawwal A Nijeriya
  • Rikici ya ɓarke bayan wata mata ta mari ɗan sanda a Saudiyya
  • JIBWIS Giwa Ya Bukaci Al’ummar Yakawada su Rike Darussan Al-Qur’ani