Falalar Ramadan: Wata na rahama, gafara, da tsira daga wuta
Published: 1st, March 2025 GMT
Azumin watan Ramadan na daga cikin shika-shikan Musulunci, kuma Allah ne Ya wajabta shi a kan bayinsa.
Wannan wata yana da falala da lada mai yawa, domin Allah Ya keɓe shi da girma da ɗaukaka.
Ga wasu daga cikin falalar azumin watan Ramadan:
1. Ana buɗe kofofin Aljanna, ana rufe ƙofofin wuta, kuma ana ɗaure shaiɗanu.
2. Yin azumi da tsayuwar sallar Tarawihi saboda Allah da neman lada, ana gafarta zunuban bawa da suka gabata.
3. Akwai daren Lailatul-Kadari, wanda ya fi wata dubu daraja. Duk wanda ya yi ibada a wannan dare yana mai imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa na baya.
4. Yin Umara a watan Ramadan yana daidai da yin aikin Hajji tare da Manzon Allah (SAW).
5. Watan Ramadan wata ne na Alƙur’ani, saboda a cikinsa aka saukar da shi. Don haka, ya dace a yawaita karanta shi.
6. Watan Ramadan wata ne na kyauta, ciyarwa da sadaka. Manzon Allah (SAW) ya fi yawan kyauta a wannan wata.
7. Baccin mai azumi ibada ne, domin yana rage sha’awa da kula da zuciya.
8. Mai azumi yana da farin ciki biyu:
Yayin da zai buɗe baki bayan azumi. Lokacin da zai haɗu da Allah (S.W.A.) ranar alƙiyama.9. Azumi garkuwa ne daga wutar Jahannama. Yana kare mutum daga sharrin sha’awa da zunubi.
10. A Ramadan, Allah Yana ’yantar da bayinsa daga wuta. Duk wani dare, Allah Yana yafe wa bayinsa kuma yana kuɓutar da su daga azabar lahira.
Wannan wata mai albarka yana ƙarfafa imani, ibada, da kyautatawa.
Don haka, ya kamata Musulmi su yi amfani da watan Ramadan don samun kusanci ga Allah da aikata kyawawan ayyuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kyautatawa Manzon Allah SAW Ramadan watan Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare
Gwamnatin Nijeriya ta sanar da dakatar da tsarin bai wa ɗalibai tallafi domin samun damar zuwa ƙetare ƙarin ilimi.
Ministan Ilimi, Tunji Alausa, shi ne ya sanar da wannan mataki, da ke nufin cewa za a kawo ƙarshen wannan tsari da aka share tsawon shekaru ana aiwatarwa.
Yadda yara 5 suka mutu a cikin motar da aka yi watsi da ita Yadda rashin wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitociMista Alausa ya bayyana cewa wannan matakai ya samu ne sakamako nazari da aka yi wajen sanya ƙaƙƙarfan jari a manyan makarantun ƙasar.
Ministan ya ce daga yanzu babu batun bai wa ’yan ƙasar kuɗaɗen ƙaro ilimi daga ƙetare, saboda yanayi da ake ciki da ma kyawun tsari da ake da shi a cikin ƙasar.
A cewarsa, dukkannin kwasa-kwasan da ’yan Nijeriyar ke zuwa wasu ƙasashen domin nazarin su, akwai su a cikin jami’o’i da ma kwalejojin fasaha masu nagarta da ake da su.
Ministan ya ce kuɗaɗen da ake kashewa wajen daukar nauyin karatun ɗaliban a ƙetare, zai fi dacewa a sanya su wajen inganta jami’o’in da kwalejojin da ake da su.
Sanarwar na zuwa ne a yayin da Hukumar Bunƙasa Arewa maso Yamma NWDC ta soke bayar da tallafin karatu ga ɗaliban da suka fito daga yankin.
Makonni kaɗan da suka gabata ne Hukumar ta NWDC ta fitar da sanarwar cewa tana neman haziƙan ɗalibai da suka fito daga yankin domin ɗaukar nauyin karatunsu a wasu ƙasashe ƙetare.
Sai dai wata sanarwa da hukumar ta fitar safiyar wannan Juma’ar, ta ce an soke tsarin, inda za ta mayar da hankali kan wasu ababen domin bunƙasa yankin.