Mece Ce Makomar ‘Ramadan Basket’ A Wannan Lokaci Na Matsin Tattalin Arziki?
Published: 1st, March 2025 GMT
Sunana Aisha T. Bello daga Jihar Kaduna:
Rashi ramadan basket nasa a kore saurayi saboda ‘yan mata sun maida ramadan basket dole. Shawara ta ga al’ummar musulmi duniya shi ne; mu yi amfani da wannan dama gun rokon Allah, saboda in Allah ya nuna mana wanan mu gani ba lallai bane mu ga wani watan Ramadan din ba, kuma mu sa kasar mu cikin addu’a Allah ya bamu dacewa.
Sunana Abubakar Ahmad, daga Jihar Nassarawa:
Ga me hali ya kan shiryawa gajiyayyu marasa hali, wanda kuma Allah bai hore masa ba ya shiga sahun wanda sai dai a dauka a basu su wadannan ba sa shirya komai face yawan salloli da addu’o’i da neman taimakon ubangiji Allah ya fitar da su daga kangin talauci da suka samu kansu a ciki. A halin da ake ciki ramadan basket yana natukar wahala, tsakanin ‘yan mata da samari za a yi ta samun matsala a wannan lokacin, amma idan har soyayya ce ta gaskiya ya kamata ita budurwar ta fuskanci halin da ake ciki tayi hakuri ga dukkanin abin da ya samu, wani koda yanada halin yi akwai dawainiya da yayi masa yawa na iyaye ko ‘yan’uwa, ko kanne ko wata bukata ta kansa wacce yake ganin tafi mahimmanci a kan ramadan basket din.
Sunana Hassana Aminu Zubairu daga Jihar Kano:
A gaskiya duk wani musulmi kwarai yana shiri kafin gabatowar watan ramadan ,ya shirya wa ransa zai jajirce wajen bautar ubangiji domin neman kusanci da ubangiji. Yawan ci ‘yan mata suna shirin yin ibada da rokar miji nagari, wasu kuma suna shirin da karbar ramadan basket daga wajen samarinsu,haka suma samari wasu suna shirin ibada da rokar mace tagari sannan kuma wasu suna shirin farantawa yanmata su da ramadan basket. Ramadan basket ta wani fannin yana da amfani, domin farantawa dan uwanka musulmi yana da babban lada to, amma kuma ta wani fannin ba shi da amfani saboda yana zama kamar gasa ko karya, wane yayi abu kaza ni kuma na kere shi nayi wanda ya fi shi to, a gaskiya indai dan gasa za ai ko dan karya to a gaskiya gwara a hakura ba a yi ba.
Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:
To da farko shirin da aka yi wa wannan wata mai alfarma shi ne Allah ya nuna mana shi muna cikin masu rai da lafiya, bangaren kuma tanaji mun yi iya bakin gwargwado duba da irin halin da ake ciki na matsin tattalin arzikin dama tsadar rayuwa. To magana gaskiya batun Ramadan basket wani abu ne da idan mutum yana da hali babu laifi sai ayi amma idan babu hali sai ayi domin ana cikin wani yanayi na matsin tattalin arzikin da tsadar rayuwa abubuwa da dama da aka saba yi yanayi ya jawo an hakura da su. To amfanin sa kyautatawa ce a tsakanin masoya don haka idan da hali babu laifi sai ayi idan kuma babu hali sai ayi hakuri yau da gobe sai Allah. Sawara dai a nan ita ce; wannan wata ne mai alfarma na ibada don haka ya kamata mu dage da ibada da ayyuka nagari domin mu dace da falalar sa da kuma addu’a tukuru domin Allah ya kawo mana karshen matsalolin da suka addabi kasar mu Najeriya baki daya.
Sunana Abubakar Usman Malam Madori:
Mukan zabi abun da ya fi muhimmaci mu bar wanda ba shi da muhimmaci ko kuma mai muhimmacinma, mu rage masa karfi, domin sassauta rayuwar mu da ta iyalanmu musamman a wannan wata namu mai albarka. Domin yin rayuwa daidai ruwa daidai tsaki. ‘Yanmata da samari da ma’aurata sukan sa ran dan wani abu na kyautatawa daga wajen masoyansu ta hanyar ba da (Ramadan Basket). Su ma samarin sukan sa ran kayan bude baki daga wajen ‘yanmatan su. To ina kira ga samari da ‘yanmata da ma’aurata da ku tsaya a inda Allah ya aje ku kada ku yi abun da za ku takura kanku, kowa ya san halin da ake ciki na babu, idan akwai ayi dai-dai karfi idan kuma babu a hakura.
Sunana Hafsat Yusuf daga Karamar Hukumar Isa A Jihar Sokoto:
Yanayi baya hana mutane tattali da shiri domin watan Ramadan, sauki a wurin Allah yake. Al’adar Ramadan basket za ta yi kasa sosai, saboda dawainiyar za ta yi nauyi sosai duba da yanayin da ake ciki na tsadar rayuwa, babu amfani ga yin ramadan basket saboda wasu mutanen sukan yi abun da ya fi karfinsu saboda a yabe su, daga karshe ina ba ‘yan uwa shawarar kulawa da ibadun watan Ramadan da kuma yawan yin istigfari.
Sunana Sa’idu Suleman Malam Madori A Jihar Jigawa:
To a takaice dai na yi shiri na watan Ramadan wajen koyi da fiyayyen halitta da dukufa wajen bautawa mahalicci domin neman ‘yantuwa a wajen Ubangiji. ‘Yanmata sun yi shiri tsaf domin amsar Ramadan basket kamar yadda suke fada yayin da samari suma sun shirya wajen bayarwa duk da dai yanayin matsi da karancin kudade a hanun al’ummah. Haka magidanta suna shirye-shirye domin kyautatawa ga iyalansu, makomar ramadan basket a takaice dole ta canja zani ba kamar baya ba duba da yanayin rayuwa da tattalin arziki, Suma mata dole su yi hakuri da yadda suka samu. To amfanin ramadan basket bai wuce kara dankon soyayya a tsakanin samari da ‘yanmata ba musamman a wannan yanayi da ake ciki, hakan kyautatawa ne kwarai.
Sunana Alh Ahmad Salisu daga Karamar Hukumar Isa, Jihar Sokoto:
Mun shirya tsaf domin zuwan azumin watan Ramadan da abubuwa daban-daban, ramadan basket yanada kyau idan saurayi ya kyautatawa budurwanshi da ababuwan mure rayuwa. Shawarata ga al’umma ita ce mu yawaita karatun Al-kur’an da azkar da sadaka.
Sunana Usman Adamu Malam Madori A Jihar Jigawa:
Shirye-shiryen da ake yi ba kamar irin na lokacin daya shude ba, domin lokacin daya shude a saukake ake yin shirin amma yanzu ana fama sosai Allah ya dafa mana Amin. ramadan basket yana da matukar mahimmaci a tsakanin masoya ko kuma bestie saboda yana kara dankon mu’amala ta kasantuwar juna. Sai dai kuma mun tsici kanmu a wani irin yanayi na tsananin tsadar rayuwa wanda ba kowa bane zai iya yin wannan hidimar ta ramadan basket a wannan lokacin bisa yanayin aljihunan samarin sun yi low mata a yi hakuri.
Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Rano LGA Jihar Kano:
Niyyar ibada da kara kaimi wajen addu o i domin samun saukin wannan kuncin rayuwar da muke ciki. Gaskiya babu wani tasiri da zai yi duba da yanzu koda kasuwanci ka ke yi abin yayi baya (ciniki) sannan kuma ga tsadar kayyakin da ake yi domin gabatar da wannan kyauta din.
Sunana Muh’d Uba:
Gaskya idan muka duba abin da addini ya shawarci al’umma game da almubazarancin dukiya, sannan duba ga halin da ake ciki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Ramadan Basket Tattalin Arziƙi Ramadan basket ramadan basket watan ramadan tsadar rayuwa watan Ramadan
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta
Kamar yadda ba a lokaci guda a ke gina dabi’u ba, haka nan ba zai yiwu a rusa su a lokaci guda ba. mutum na gina dabi’a ne ta hanyar yin mu’amala da mutane. Gina dabi’un na farawa daga shekarun yarinta, saboda a sannan ne a ke koyon al’adu, tarbiyya da girmama manya. Har zuwa mutuwan mutum ya na mu’amala ne da mutane ya na gina sabbin dabi’u.
Iyaye su ne ke ginawa yara dabi’un farko, shi ne ma ya sa a ke so su rika kiyaye irin maganganun da za su rika yi a gaban yaransu, sannan su tsaftace mu’amalolinsu ta yadda yaran ba za su rika kwaikwayon abubuwan da ba su dace ba. hatta da yin dakuwa da nufin zagi, a wurin iyaye yara ke fara koyo. Shi ne ya sa za ka ga wani ya zama gwani a zagi, kwararren gaske. Ba a sama ya samo dabi’ar ba, abin da ya taso ya ga a na yi a gidansu kenan. Wasu kuwa gidansu mutanen kirki ne, don haka ba su iya samun daman kwaikwayon zagi a gida.
Daga gida, lokacin da yaro ya fara wayo, ma’ana zai yiwu a kyale shi ya rika fita waje, sannan ya kai shekarun fara zuwa makaranta. Wasu unguwarsu ‘G.R.A’ ne, babu hayaniya; ba irin unguwannin nan ba ne da a ke cakude da juna. A nan, dabi’un yaransu sun fi samuwa a mu’amalar da yaran ke kwaikwayo daga iyaye.
A irin unguwannin da a ke cakude, ma’ana wadanda yawanci ma gidajen haya ne masu mutane rututu, ya na wahala a iya saita dabi’un yaro. Na farko yaro zai rika kwaikwayon dabi’un iyayenshi, sannan zai rika kwaikwayon na ‘yan hayan gidansu, sannan zai rika kwaikwayon na sauran yaran kan layi; da ya ke irin wannan unguwannin kofofi a bude su ke, yaro ko da rarrafe ya ke yi, zai iya fita kan layi. Wasu yaran ma, dabi’un da su ke kwaikwayo wa a kan layi, ya fi karfin sanin iyayensu. A irin wadannan unguwannin mutane sun fi saurin diban dabi’u, masu kyau da marasa kyau.
Idan yaran wadanchan unguwannin ‘G.R.A’, suka fara zuwa makaranta, za su iya haduwa da yaran unguwannin da a ke cakude da juna. A makaranta za su fara musayar dabi’u a tsakanin juna. Mutum ya na kwance a gida, ya yi tsammanin dabi’unshi da na matarshi da mutanen cikin gida kadai dansu ke kwaikwaya, bai san cewa ya na kwaikwayo wasu daga mu’amalarshi da wasu yara a makaranta ba. wannan na faruwa hatta a makarantun Islamiyyoyi.
Ba kawai a yarinta a ke gina dabi’u ko kwaikwayonsu ba, kowanne mataki na rayuwa a na sake kwaikwayon dabi’u ne da gina sabbi. Wani zai taso har ya balaga da dabi’u masu ban sha’awa da burgewa, amma da zaran ya fara makarantar Sakandare ko gaba da Sakandare, sai yanayin mu’amalarsa ta chanza, saboda haduwa da zai yi da wasu sabbin mutane wadanda suka fito daga wurare mabambanta. Idan ba a yi sa’a ya hadu da abokan arziki ba, sai ya hadu da wadanda a hankali za su gina mishi dabi’un shaye-shaye, ko kuma neman mata.
Musamman a jami’o’i, wata yarinyar za ta zo daga gidansu da dabi’un kwarai, babu ruwanta da sa suturar banza. Yawancin irin wadannan ‘yan matan, a kan hada su zama dakin ‘Hostel’ daya da su. Tun kafin ta fara halartan azuzuwa don daukan darasi, tun kafin ta san sauran mutanen ajinsu, da wadannan abokan zaman nata za ta fara mu’amala. Idan ba a dace ba, a hankali za su koya mata dabi’ar fita babu lullubi ballantana hijabi. Idan samarinsu sun zo zance, sai su rika takura mata a kan ta yi musu rakiya, har watarana abokin saurayin ya ganta ya ce ya na so, shi kenan ita ma ta shiga shirgin.
Kowacce irin dabi’ar mutum, idan a na son a rusa ta, ba a garaje, ba a gaggawa, ba kuma a nuna kosawa. A hankali za a rika nunawa wannan dabi’ar rashin dacewarta, da kuma nakasunta. Ba a rusa dabi’a da karfi ko da fada, ba a rusa ta da iko ko nuna isa. Dabi’u sun fi bukatar lalama da sassauci.
Kafin ka iya rusa dabi’ar mutum, dole sai ka yi nazarin yadda ya ke kallon wannan dabi’a ta sa, ma’ana fahimtarsa dangane da dabi’ar. Idan Yaro ne wanda ke shaye – shaye, dole ne sai ka fahimci menene fahimtarsa dangane da shaye-shaye, tare da nazarin abubuwan da suka jefa shi zuwa ga shaye – shayen. Shin akwai wani abu da ya ke kauna? Idan akwai menene wannan abin? Shin ya na samun daman yin tunani, wanda ba a maye ba, a hankalinshi? Idan ya kan samu lokacin yin tunani ba tare da ya sha komi ba, sai ka fahimci wannan lokacin, a sannan ne za a iya fara aikin chanza mishi tunani.
Kafin mutum ya fara wannan dabi’a da a ke son rusawa, dole a baya ya na da wasu dabi’u, kuma ya na da wasu abokai wadanda a bayan ya ke mu’amala da su. Dole a na bukatar sannan wannan. Saboda idan dabi’ar ta yi kamari, dole ne sai an sake dawo mishi da rayuwar da ya yi a baya, an dawo mishi da tsofaffin abokai, sannan a shimfida musu tsarin yadda za su tafiyar da mu’amala a tsakaninsu, idan a ka bi matakan yadda suka dace a kan yi nasarar rusa dabi’ar da ba a so. Sai dai hanzari ba gudu ba, kwaikwayon dabi’a ya fi sauri a kan rusa ta.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp