Aminiya:
2025-03-01@18:29:54 GMT

An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe

Published: 1st, March 2025 GMT

Gwamnatin Yobe ta raba wa ma’aikatan gona babura guda 200 domin gudanar da ayyukan kula da harkokin noma a jihar.

Kwamishinan ma’aikatar gona da albarkatun kasa, Ali Mustapha Goniri ne ya bayyana haka a lokacin da yake miƙa baburan ga waɗanda suka rabauta.

Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa Yadda ake ‘Spring rolls’

Ya ce an yi rabon baburan ne domin tallafa wa ayyukan ma’aikatan da kuma bunƙasa noman zamani a jihar ta hanyar sabbin dabaru da kayan aiki.

Goniri ya ce ma’aikatar gona za ta sa ido kan yadda ma’aikatan da ke aikin faɗaɗa ayyukan noma ke yi domin tabbatar da cewa manoma a kowane lungu da saƙo na jihar suna noman amfanin gona da iri masu inganci.

A cewarsa, an horas da ma’aikatan da za su yi aiki domin kyautata alaƙa tsakanin masu bincike da manoma, don haɓaka samar da kayayyaki, tabbatar da samar da abinci, da kuma inganta rayuwar manoma.

A nasa jawabin, babban sakataren ma’aikatar, Muhammad Inuwa Gulani, ya ce jami’an ma’aikatar aikin gona za su taimaka wa manoma wajen yanke shawara kan kirkire-kirkire da fasaha kan harkokin noma na zamani.

Ya ce ma’aikatan za su kuma taimaka wa manoma wajen samun sabbin bayanai da fasahohin zamani, inda ya ce shirin zai taimaka wa manoman wajen inganta sana’o’insu, da inganta rayuwar su, da tabbatar da samar da abinci ga al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babura Jihar Yobe

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje

Ya kuma kara da cewa, gwamnatin jihar Kano ta bai wa ilimi fifiko, wanda Kano ce a gaba wajen ware kasafin kudi mai yawa a shekarar 2024 da 2025 a fannin Ilimi. Bugu da kari, gwamnatin ta ayyana dokar ta-baci a fannin ilimi domin tabbatar da matasa sun samu ingantaccen ilimi wanda zai ba su damar yin fice a tsakanin takwarorinsu.

 

Da yake magana tun farko, Gautier Mignot, jakadan Tarayyar Turai a Nijeriya da ECOWAS, kuma jagoran tawagar, ya bayyana cewa, sun zo Kano ne domin halartar bikin baje kolin karatu na Turai da aka shirya yi a ranar 27 ga Fabrairu, 2025 a jihar.

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Tsaron Jama’ar Sin Na Matukar Adawa Da Barazanar Da Amurka Ta Yi Na Karin Haraji
  • Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250
  • Japan Ta Kirkiro Da Sabuwar Kimiyyar Samar Da Ingantacciyar Madarar Shanu
  • Kwara ta Raba Littafai Fiye da Dubu 74 Kyauta Ga Dalibai
  • Jigawa Ta Kebe Wuraren 57 don Kare Rikicin Manoma da Makiyaya
  • Gwamnatin Kano Za Ta Ɗau Nauyin Ɗalibai 1,002 Domin Karatu A Ƙasashen Waje
  • CICPE Karo Na 5 Zai Mayar Da Hankali Kan Kirkire-Kirkiren Fasahohin Zamani
  • Me Sabon Karfin Samar Da Ci Gaban Ayyukan Gona Zai Kawo Mana?
  • Gidauniyar Sarki Salman Ta Rab Tallafin Abinci Ga Mutane 2,450 A Kebbi