Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-02@12:33:43 GMT

Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria

Published: 2nd, March 2025 GMT

Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria

Malamai daga makarantun firamare 116 dake karamar hukumar Zaria sun gudanar da taron addu’o’i na musamman ga shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen da gwamnatin jihar Kaduna.

Malaman sun gudanar da addu’o’in ne domin nuna farinciki da godiya bisa yadda suke matukar kula da ilimi,wanda hakan ya inganta harkokin ilimin kuma ya kara bunkasa jin dadin Malaman yankin.

Sakatariyar ilimi ta karamar hukumar Zaria, Dr Hassana Lawal ta shedawa manema labaru lokacin addu’o’in a zaria cewa a kalla Malaman makarantun firamare 2,225 ne suka amfana da tallafin kayan abinci domin gudanar da azumin watan Ramadan.

A cewar ta,kayan abincin sun hada da kilo 25 na shinkafa da lita 4 na man gyada da fakitin tafiya da kuma kilo 10 na buhun garin samabita.

“Wannan shine karo na 8 da shugaban majalisar wakilan ya baiwa malaman makarantar firamaren irin wannan tallafin tun daga lokacin da hau karagar shugabancin majalisar.

“Baya ga tallafin kayan abinci,ya baiwa duk shugabannin makarantun firamare 116 da ke yankin kyautar babura domin saukaka masu zuwa wurin aiki,wanda a cewar ta abin godiya ne matuka”.

Haka kuma sakatariyar ilimin ta yaba da kokarin da gwamnan jihar kaduna, Malam Uba Sani ke yi na bunkasa ilimi a jihar.

Dr Lawal ta ce kokarin da gwamnan ke yi sun kushi gina ajujuwa 12 a makarantun firamare da dama a karamar hukumar Zaria baya ga tallafin kayan karatu, wanda hakan ne yasa dole su yi masu addu’o’in.

Ta kara da cewa Malaman sun zami watan Ramadan ne domin gudanar da addu’o’in Allah ya baiwa shugaban majalisar wakilai da sauran masu ruwa da tsaki a harkar ilimi nasara da kwarin gwiwa wajen ci gaba da bunkasa ilimi a jihar.

A nashi jawabin, sakataren Kungiyar malamai na karamar hukumar Zaria, Malam Kasimu Mohammed ya ce tallafin kayan abincin ya taimaka wa Malaman matukar gaske.

A don haka sai ya bukaci sauran yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi shugaban majalisar wakilan ta hanyar tallafawa Malaman makarantun firamare a yankunan su.

Haliru Hamza

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Furame Zaria karamar hukumar Zaria makarantun firamare shugaban majalisar tallafin kayan

এছাড়াও পড়ুন:

Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano

Rundunar ’Yan Sandan Kano, ta kama wani matashi bisa zargin kashe jami’in tsaron sa-kai a filin Idi yayin hawan sallah ƙarama.

A cewar sanarwar da ’yan sanda suka fitar, matashin mai shekara 20, ya daɓa wa jami’in wuƙa yayin da yake aiki tare da tawagar Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, bayan sallar Idi a ranar Lahadi.

Farashin fetur ya ƙaru sakamakon hana Dangote mai a Naira Babu tsamin dangantaka tsakaninmu da Gwamnan Sakkwato — Sarkin Musulmi

Haka kuma, wani jami’in sa-kai ma ya ji rauni kuma yana jinya a Asibitin Murtala Muhammad da ke Kano.

Rundunar ’yan sandan ta ce ta fara bincike kan lamarin, kuma ta gayyaci Shamakin Kano, Alhaji Wada Isyaku, domin amsa tambayoyi.

A baya-bayan nan, ’yan sanda sun hana gudanar da Hawan Sallah a Kano, yayin da ake ci gaba da rikicin sarauta tsakanin Muhammadu Sanusi II da Aminu Ado Bayero.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna samun galabar daƙile kwararowar baƙin haure — Jamus
  • Sojojin Yemen Sun Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kataparen Jirgin Ruwan Yaki Mai Daukar Jirage Na kasar Amurka
  • Shugaban Tinubu Ya Tube Kyara A Matsayin Shugaban Kamfanin NNPC Ya Kuma Sannan Ya Maye Gurbinsa
  • Tsohon Gwamnan Zamfara Ya Bukaci A Ci Gaba Da Tallafawa Mabukata Bayan Ramadan.
  • Gaza : Fiye da mutane 1,000 Isra’ila ta kashe tun daga ranar 18 ga Maris
  • Sani Ahmad Lere Na Radio Nijeriya Kaduna Ya Zama Falakin Lere
  • Nijar ta fice daga rundunar MNJTF mai yaƙi da masu iƙirarin jihadi
  • Gwamna Umar Namadi Ya Taya Al’ummar Musulmi Murnar Bikin Sallah Karama
  • Eid-el-Fitr: Sarkin Kauru Ya Gargadi Masu Bai Wa ‘Yan Ta’adda Bayanai
  • Matashi ya kashe jami’in tsaron Sarki Sanusi II a Kano