Malaman Furanare 116 Sun Gabatar da Addu’o’i a Zaria
Published: 2nd, March 2025 GMT
Malamai daga makarantun firamare 116 dake karamar hukumar Zaria sun gudanar da taron addu’o’i na musamman ga shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen da gwamnatin jihar Kaduna.
Malaman sun gudanar da addu’o’in ne domin nuna farinciki da godiya bisa yadda suke matukar kula da ilimi,wanda hakan ya inganta harkokin ilimin kuma ya kara bunkasa jin dadin Malaman yankin.
Sakatariyar ilimi ta karamar hukumar Zaria, Dr Hassana Lawal ta shedawa manema labaru lokacin addu’o’in a zaria cewa a kalla Malaman makarantun firamare 2,225 ne suka amfana da tallafin kayan abinci domin gudanar da azumin watan Ramadan.
A cewar ta,kayan abincin sun hada da kilo 25 na shinkafa da lita 4 na man gyada da fakitin tafiya da kuma kilo 10 na buhun garin samabita.
“Wannan shine karo na 8 da shugaban majalisar wakilan ya baiwa malaman makarantar firamaren irin wannan tallafin tun daga lokacin da hau karagar shugabancin majalisar.
“Baya ga tallafin kayan abinci,ya baiwa duk shugabannin makarantun firamare 116 da ke yankin kyautar babura domin saukaka masu zuwa wurin aiki,wanda a cewar ta abin godiya ne matuka”.
Haka kuma sakatariyar ilimin ta yaba da kokarin da gwamnan jihar kaduna, Malam Uba Sani ke yi na bunkasa ilimi a jihar.
Dr Lawal ta ce kokarin da gwamnan ke yi sun kushi gina ajujuwa 12 a makarantun firamare da dama a karamar hukumar Zaria baya ga tallafin kayan karatu, wanda hakan ne yasa dole su yi masu addu’o’in.
Ta kara da cewa Malaman sun zami watan Ramadan ne domin gudanar da addu’o’in Allah ya baiwa shugaban majalisar wakilai da sauran masu ruwa da tsaki a harkar ilimi nasara da kwarin gwiwa wajen ci gaba da bunkasa ilimi a jihar.
A nashi jawabin, sakataren Kungiyar malamai na karamar hukumar Zaria, Malam Kasimu Mohammed ya ce tallafin kayan abincin ya taimaka wa Malaman matukar gaske.
A don haka sai ya bukaci sauran yan siyasa da masu hannu da shuni da su yi koyi shugaban majalisar wakilan ta hanyar tallafawa Malaman makarantun firamare a yankunan su.
Haliru Hamza
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Furame Zaria karamar hukumar Zaria makarantun firamare shugaban majalisar tallafin kayan
এছাড়াও পড়ুন:
Motar hatsi kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
Hatsarin mota ya yi ajalin mutum biyar tare da jikkatar wasu takwas a yayin da suke bikin Ista a garin Billiri da ke Jihar Gombe.
Hatsarin ya faru ne a safiyar ranar Litinin, lokacin da direban wata babbar mota mai ɗauke da buhunan hatsi daga Jihar Adamawa ya auka kan dandazon jama’a da ke tsaka da shagalin bikin Ista.
An jingine wasanni a Italiya saboda mutuwar Fafaroma Francis An kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a BauchiA wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na ‘yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi ya fitar, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun yi gaggawar kai ɗauki, inda suka kwashe waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.
Sanarwar ta kuma ce bayan faruwar hatsarin, wasu fusatattun matasa sun cinna wa motar wuta tare da sace kayayyakin da ta ɗauko.
“Lokacin da ‘yan sanda suka kai ɗauki, matasan sun yi musu ruwan duwatsu, sai dai an shawo kan lamarin, kuma an dawo da zaman lafiya a yankin.”
Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Gombe, Bello Yahaya, ya bayyana jimami kan faruwar lamarin tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan.
Shi ma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammad Inuwa Yahaya, ya bayyana damuwa kan wannan iftila’i.
A cikin wata sanarwa da Babban Daraktan yada labarai na gidan gwamnati, Isma’ila Uba Misilli ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa lamarin abu ne mai girgiza zuciya.
Gwamnatin jihar ta yi alƙawarin ɗaukar nauyin magani ga waɗanda suka ji raunuka, tare da tabbatar da cewa za a ɗauki matakan kare faruwar irin wannan matsala a nan gaba.