Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC
Published: 2nd, March 2025 GMT
Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta ce ita ce ta kai samame otal ɗin White Hill da ke kan titin Shiroro a Minna, Babban Birnin Jihar Neja.
A yayin farmakin, an kama aƙalla baƙi 10 da ake zargi da aikata damfara a Intanet, wanda aka tafi da su Kaduna.
Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren Dankali Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a EdoWani ma’aikacin otal ɗin da ya nemi a sakaya sunansa, ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar ’yan bindiga ne suka yi basaja a kayan EFCC, sula sace baƙi 10 a ranar 27 ga watan Fabrairu.
“Ba ’yan bindiga ba ne. Jami’an EFCC ne suka zo suka kama wasu ‘yan damfara suka tafi da su Kaduna,” in ji shi.
Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya kuma yi watsi da wannan jita-jitar.
Ya shawarci ’yan jarida su tuntuɓi EFCC domin tabbatar da sahihancin lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan damfara
এছাড়াও পড়ুন:
Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha
Mijin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Emmanuel Oritsejolomi Uduaghan, ya bayyana cewa matarsa ta taɓa kawo masa ƙorafi game da cin zarafin da ta ce Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya yi mata.
A cewarsa, rikicin ya fara tun lokacin da Natasha ta tsaya takarar kujerar Sanata a 2019 a ƙarƙashin jam’iyyar SDP, inda ta nemi kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya.
Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC Hisba ta kama wasu matasa ba sa azumi a KanoA lokacin, Akpabio yana riƙe da mukamin Ministan Neja Delta.
“Da kaina na je na same shi na buƙaci ya bai wa matata girman da ta cancanta, sannan ya girmama abotar da ke tsakaninmu.
“Bayan mun tattauna sai muka amince da a warware maganar cikin mutunci,” in ji shi.
Bayan zaɓen 2019, Natasha ta sake tsayawa takarar Sanata a 2023 a ƙarƙashin jam’iyyar PDP, inda ta samu nasara.
A lokacin, ana raɗe-raɗin cewa Akpabio bai ji daɗin yadda ta samu goyon baya ba, kuma hakan ya ƙara haddasa rashin jituwa a tsakaninsu.
“Amma bayan maganar da muka yi, sai matata ta ci gaba da bayyana damuwa game da irin cin zarafin da ta ke fuskanta daga shugaban majalisar.
“Ni dai na yarda da matata, kuma aure muka yi na soyayya da ƙauna. Babu abin da ya fi min ita a yanzu domin ita ce farin cikina.”
Natasha dai ta ce tana da wasu hujojji da za ta fitar, wanda ke nuna yadda Akpabio ya neme ta, lamarin da yanzu haka ya haifar da zazzafar muhawara a Najeriya.