Aminiya:
2025-04-23@06:06:38 GMT

Mu ne muka kai samame otal ba ’yan bindiga ba — EFCC

Published: 2nd, March 2025 GMT

Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta ce ita ce ta kai samame otal ɗin White Hill da ke kan titin Shiroro a Minna, Babban Birnin Jihar Neja.

A yayin farmakin, an kama aƙalla baƙi 10 da ake zargi da aikata damfara a Intanet, wanda aka tafi da su Kaduna.

Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren Dankali Fasinjoji 12 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Edo

Wani ma’aikacin otal ɗin da ya nemi a sakaya sunansa, ya musanta jita-jitar da ake yaɗawa cewar ’yan bindiga ne suka yi basaja a kayan EFCC, sula sace baƙi 10 a ranar 27 ga watan Fabrairu.

“Ba ’yan bindiga ba ne. Jami’an EFCC ne suka zo suka kama wasu ‘yan damfara suka tafi da su Kaduna,” in ji shi.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya kuma yi watsi da wannan jita-jitar.

Ya shawarci ’yan jarida su tuntuɓi EFCC domin tabbatar da sahihancin lamarin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan damfara

এছাড়াও পড়ুন:

An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja

Gwamna Umar Mohammed Bago, ya sanya dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 12 a birnin Minna na Jihar Neja.

Wannan dai na zuwa ne sakamakon hare-haren da ya janyo salwantar rayuka da aka samu a bayan nan a babban birnin.

Hanyoyin da za a magance rikicin Filato — Masana HOTUNA: Yadda Pantami ya kai wa Sheikh Jingir ziyarar ta’aziyya

A cewar gwamnan, an haramta zirga-zirgar baburan ’yan acaɓa da masu Keke Napep daga ƙarfe 6 na yamma zuwa 6 na safiyar kowacce rana.

Gwamnan ya bayyana hakan a yayin wani taro na musamman da ya gudana da masu ruwa da tsaki kan sha’anin tsaro da ya ƙunshi sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro a Fadar Gwamnatin jihar a ranar Talata.

A yayin da dokar ba ta shafi duk wata buƙatar lafiya ta gaggawa, Bago ya ce ba a buƙatar ganin ababen hawa daga lokacin da dokar ta fara aiki da zummar daƙile matsalar tsaro da babban birnin ke fuskanta.

Ya jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta zuba ido a yayin da miyagu ke ci gaba da kai hare-hare da kashe mutanen da ba su ji ba kuma ba su gani ba.

Ya umarci dukkan dagatai da masu unguwanni da su tabbatar da ɗaukar bayanan duk wasu baƙi da suka shigo yankunansu.

Kazalika, ya yi gargaɗin cewa duk gidan da aka kama yana bai wa miyagu mafaka ko masu fataucin muggan ƙwayoyi za a rushe shi.

A ’yan kwanakin nan dai birnin Minna na fuskantar matsalar tsaro da ta haɗa da dabanci, hare-hare da kisan kai da sauran miyagun ababe masu ɗaga hankalin mazauna.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Neja Ta Saka Dokar Zama A Gida A Minna
  • An sanya dokar hana fita ta sa’o’i 12 a Neja
  • Motar hatsi ta kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Motar hatsi kashe masu bikin Ista 5 a Gombe
  • Bikin Ista: Hatsarin mota ya laƙume rayuka 5 a Gombe
  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja
  • An Yi Mummunar Arangama Da ‘Yan Bindiga A Sakkwoto
  • NDLEA Ta Kama Masu Sayar Da Kwaya Ga Ƴan Bindiga A Kano
  • Najeriya : Mutum 56 suka mutu a harin Benue