’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi
Published: 3rd, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Bagiza da Rausa Kade a Ƙaramar Hukumar Arewa, Jihar Kebbi, inda suka kashe mutum shida a makon da ya gabata.
Maharan sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, sannan suka hallaka ɗaya a Bagiza yayin harin da suka kai domin satar shanu.
Matata ta taɓa kawo min ƙarar Akpabio — Mijin Natasha Girke-girken Azumi: Yadda ake yin Tsiren DankaliWannan ta’addanci ya jefa mazauna yankin cikin tsananin fargaba.
Gwamna Nasir Idris ya bayar da tabbacin inganta a tsaro jihar.
Ganin yadda mutane ke cikin tsoro, Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya kai ziyarar jaje ƙauyukan a ranar Asabar.
Ya tabbatarwa da al’ummar yankin cewa gwamnati na aiki tuƙuru domin shawo kan matsalar tsaro, musamman a yankin Kebbi ta Kudu.
Gwamnan ya bayyana cewa mafi yawan hare-haren da ake fuskanta a Kebbi na zuwa ne daga maƙwabtan jihohi.
“Tun daga lokacin da muka hau mulki, muna ɗaukar matakan da suka dace domin magance matsalar tsaro, kuma muna samun ci gaba.
“Rashin ɗaukar matakin gaggawa daga jami’an tsaro a wasu maƙwabtan jihohi yana bai wa ’yan bindiga damar kutsowa cikin yankunanmu suna kai hari,” in ji Gwamnan.
Ya buƙaci jami’an tsaro da su ƙara ƙaimi domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.
A yayin ziyarar, Gwamna Nasir Idris ya bayar da tallafin miliyan 10 ga iyalan waɗanda aka kashe.
Haka kuma, ya bayar da umarnin gina Masallacin Juma’a da kuma bohol guda biyu da ke amfani da hasken rana a ƙauyen Rausa Kade.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Hon. Sani Aliyu Tela, ya jinjina wa Gwamnan bisa wannan kulawa.
Ya bayyana cewa harin ya faru ne a daren Alhamis, inda ’yan bindiga suka kai farmaki domin satar dabbobi.
“Sun kashe mutum biyar a Rausa Kade, suka harbi mutum ɗaya a Bagiza. Mun yaba da kulawar da kake ba mu,” in ji shi.
Jama’a dai na fatan matakan da gwamnati ke ɗauka za su kawo ƙarshen hare-haren da suka addabi yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Gwamna Nasir hari Ƙauyuka
এছাড়াও পড়ুন:
Sabbin Haraji: Yadda ‘Yan Bindiga Ke Tilasta Wa Jama’a Biyan Miliyoyin Kuɗi A Zamfara
Garuruwan da aka fi tsananta wa harajin sun haɗa da Gijinzama da aka tilasta musu biyan Naira miliyan 8.5, Dakolo da aka karɓi Naira miliyan 5 da buhun wake 20, sai Kibari da Kunchin Kalgo da suka biya Naira miliyan 20, Sungawa da Naira miliyan 15, da kuma Yalwa da aka tilasta su biyan Naira miliyan 2.7.
Bayan rasuwar Isuhu Yellow, wani ƙasurgumin jagoran ‘yan bindiga mai suna Dogo Gide ya sa harajin Naira miliyan 100 a kan ƙauyuka 23 da ke ƙaramar hukumar Tsafe.
A ƙarshen makon da ya gabata kuma, mazauna ƙauyen Dankurmi a ƙaramar hukumar Maru sun fuskanci sabon harajin Naira miliyan 60.
Wani mazaunin ƙauyen Dan Jibga, Muhammad Dogo, ya bayyana cewa bayan kashe mutane biyu a Gama Lafiya, an ƙaƙaba wa yankin harajin Naira miliyan 10.
Haka kuma, haraji ya ci gaba da yaɗuwa a Unguwar Tofa (Naira miliyan 26.6), Makera (Naira miliyan 15), Sungawa (Naira miliyan 20), Rakyabu (Naira miliyan 7), Yalwa (Naira miliyan 8), Mai Saje (Naira miliyan 11), da Langa-Langa (Naira miliyan 20 zuwa 30).
Sauran yankunan da ‘yan bindigar suka ƙaƙaba wa haraji sun haɗa da Gidan Dawa, Rijiyar Tsakar Dawa, Dan Jibga da kuma Bilbis. Malam Ibrahim Maru, wani mazaunin karamar hukumar Maru, ya ce matsalar ta’addanci a yankin na ƙara ta’azzara fiye da da.
Lamarin na nuna irin ƙalubalen da jama’a ke fuskanta a hannun masu aikata laifuka, wanda ke buƙatar kulawar gaggawa daga gwamnati da hukumomin tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp