Aminiya:
2025-03-03@21:18:07 GMT

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki

Published: 3rd, March 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da rabon abincin buɗa-baki domin tallafa wa mabuƙata a wannan wata mai albarka na Ramadana.

Mataimakin Gwamnan Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ne ya ƙaddamar da rabon abincin a cibiyar Dandali da ke Ƙaramar Hukumar Fagge a jihar.

HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki

Bayanai sun ce gwamnatin jam’iyyar NNPP ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf da ta ƙaddamar da wannan shiri tana da burin raba abincin buɗa-baki ga mabuƙata masu azumtar watan Ramadana.

Gwamnatin ta ce an tanadi cibiyoyi 91 domin raba wa mabuƙata 91,000 abincin buɗa-baki duk rana nan da tsawon kwanaki 27 masu zuwa.

Domin tabbatar da samun nasara, gwamnatin ta ce ta ɗauki masu aikin girke-girke da za su riƙa dafawa sannan su raba wa mabuƙata abincin.

Mataimakin Gwamnan wanda shi ne ke jagorantar shirin raba abincin a bana, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka ƙaddamar da shirin, yana mai kiran waɗanda aka ɗora wa alhakin aikin su tabbatar da raba wa mabuƙata abincin a kan kari.

Aminiya ta ruwaito cewa, Mataimakin Gwamnan ya samu rakiyar wasu ƙusoshin Gwamnatin Kano wajen ƙaddamar da rabon abincin da suka haɗa da Kwamishinan Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya da Kwamishinan Harkokin Addini, Sheikh Tijjani Auwal da sauransu.

Gwamnatin Kano ta jaddada ƙudirinta na rage raɗaɗin al’umma musamman Musulmi a wannan wata mai falala.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Aminu Abdussalam Gwarzo Buɗa baki Jihar Kano Ramadan ƙaddamar da rabon abincin abincin buɗa baki Gwamnatin Kano wa mabuƙata

এছাড়াও পড়ুন:

An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe

Gwamnatin Yobe ta raba wa ma’aikatan gona babura guda 200 domin gudanar da ayyukan kula da harkokin noma a jihar.

Kwamishinan ma’aikatar gona da albarkatun kasa, Ali Mustapha Goniri ne ya bayyana haka a lokacin da yake miƙa baburan ga waɗanda suka rabauta.

Yadda farashin kayan abinci ya sauka a kasuwannin Arewa Yadda ake ‘Spring rolls’

Ya ce an yi rabon baburan ne domin tallafa wa ayyukan ma’aikatan da kuma bunƙasa noman zamani a jihar ta hanyar sabbin dabaru da kayan aiki.

Goniri ya ce ma’aikatar gona za ta sa ido kan yadda ma’aikatan da ke aikin faɗaɗa ayyukan noma ke yi domin tabbatar da cewa manoma a kowane lungu da saƙo na jihar suna noman amfanin gona da iri masu inganci.

A cewarsa, an horas da ma’aikatan da za su yi aiki domin kyautata alaƙa tsakanin masu bincike da manoma, don haɓaka samar da kayayyaki, tabbatar da samar da abinci, da kuma inganta rayuwar manoma.

A nasa jawabin, babban sakataren ma’aikatar, Muhammad Inuwa Gulani, ya ce jami’an ma’aikatar aikin gona za su taimaka wa manoma wajen yanke shawara kan kirkire-kirkire da fasaha kan harkokin noma na zamani.

Ya ce ma’aikatan za su kuma taimaka wa manoma wajen samun sabbin bayanai da fasahohin zamani, inda ya ce shirin zai taimaka wa manoman wajen inganta sana’o’insu, da inganta rayuwar su, da tabbatar da samar da abinci ga al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar Da Shirin Ciyarwar Na Watan Ramadan
  • Ya rasu a yayin buɗa-baki a Abuja
  • Ramadan: Hon Jaji Ya Ƙaddamar Da Tallafin Abinci Ga Mutane Sama Da 500,000 A Zamfara
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 a ƙauyukan Kebbi
  • ’Yan bindiga sun hallaka mutum 6 ƙauyukan Kebbi
  • Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi
  • Saudiyya Ta Raba Tan Hamsin Na Dabino A Nijeriya
  • An raba wa ma’aikatan gona babura 200 a Yobe
  • Ramadan: Saudiyya ta bai wa Kano da wasu jihohi kyautar dabino katan 1,250