Kasashen larabawa sun yi kakkausar suka ga matakin da Isra’ila ta dauka na dakatar da shigar da duk wani kayan agaji a zirin Gaza, suna masu bayyana hakan a matsayin keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da kungiyar Hamas da kuma dokokin kasa da kasa.

Ma’aikatar harkokin wajen Saudiyya a cikin wata sanarwa ta ce “Masar ta yi Allah-wadai da kuma yin tir da matakin da gwamnatin Isra’ila ta dauka na dakatar da agajin jin kai ga Gaza, tare da yin amfani da shi a matsayin wani makami na cin zarafi da azabtarwa.

Masar ta kuma yi Allah wadai da matakin da Isra’ila ta dauka na hana shigar da duk wani agajin jin kai a zirin Gaza a matsayin “ketare iyaka” na yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza.

Ma’aikatar harkokin wajen Masar a cikin wata sanarwa da ta fitar “ta yi kakkausar suka ga matakin da Isra’ila ta dauka na hana agajin jin kai da mashigin da ake amfani da shi wajen kai agaji.”

Ma’aikatar ta ce “wadannan ayyukan sun saba wa yarjejeniyar tsagaita bude wuta, dokar jin kai ta kasa da kasa, Yarjejeniyar Geneva ta Hudu, da dukkan ka’idojin addini.”

Yarjejeniyar Geneva ta hudu da aka amince da ita a shekarar 1949 bayan yakin duniya na biyu, ta ta’allaka ne kan ba da kariya ga fararen hula, ciki har da yankunan da aka mamaye.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ta dauka na

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Babban abin da suke bukata a duk wata tattaunawa shi ne a dage takunkumi

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Isma’il Baqa’i, ya jaddada cewa babban bukatar Iran a duk wata tattaunawa ita ce a dage takunkumin da aka kakaba mata ta hanyar da za ta kai ga samun sakamako mai ma’ana.

Isma’il Baqa’i ya bayyana hakan ne a yayin taron manema labarai na mako-mako da yake yi a yau litinin cewa: A kwanakin baya ministan harkokin wajen kasar Iran ya ziyarci kasar Rasha, sannan ya gana da ministan harkokin wajen kasar Italiya, a gefen shawarwari ba na kai tsaye ba tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da Amurka.

Ya kara da cewa: A gobe ne ministan harkokin wajen kasar Iran zai kai ziyarar aiki zuwa kasar China. Ya kuma kara da cewa, ana ci gaba da samun wasu ci gaba a daidai wadannan ziyarce-ziyarcen, yana mai jaddada cewa idan aka yi tambayoyi a kansu a yayin taron tambayoyi da amsa, zai ba da cikakkun bayanai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Gaza Suna Tsananin bukatar Agaji Da Kiran A Tilastawa Gwamnatin Mamayar Isra’ila Bude Mashigar Yankin
  • CONMEBOL ta buƙaci a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta 2030
  • Iran ta ce an dage tattaunawar matakin kwararru da Amurka zuwa ranar Asabar
  • Kungiyar kare farar hula ta Falasdinu ta zargi sojojin da ” kashe-kashe masu yawa”
  • Sin: Matakin Harajin Kwastam Da Amurka Ta Dauka Babakere Ne 
  • Sharhin Bayan labarai: Rage Kasafin Kudin Ma’ailatar harkokin wajen Amurka da tasirinsa
  • Tsakanin Kafa Shingaye Da Gina Gada: Yadda Matakan Amurka Da Sin Suka Bambanta Sosai
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Wasu Falasdinawa Sun Yi Shahada A Harin Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Zirin Gaza
  • Gaza : Red Crescent ta yi watsi da rahoton Isra’ila kan kisan da aka yi wa jami’an agaji