Aminiya:
2025-03-06@03:38:22 GMT

Babu abin da zai hana mu zama jam’iyya ɗaya da Kwankwaso — Shekarau

Published: 5th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kano, Mallam Ibrahim Shekarau, ya musanta cewa akwai wata ƙullaliyar gaba tsakaninsa da tsohon Gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso, inda ya bayyana cewa babu ɗaya daga cikinsu da za a iya ɗora wa alhakin haddasa saɓanin siyasar da ya shiga tsakaninsu a baya.

Cikin wani bidiyo da karaɗe dandalan sada zumunta, Shekarau ya bayyana cewa rashin jituwar da ke tsakaninsu na siyasa ya samo asali ne daga yanayi da ya fi ƙarfinsu gaba ɗaya.

“Gaskiya ni na yi imanin cewa ni da Kwankwaso ba mu da wata matsala ta zama tare a ƙarƙashin inuwar jam’iyya ɗaya. A duk abubuwan da suka faru, da ni da shi duk babu mai laifi,” inji shi.

Da yake tsokaci kan lokacin da suka yi a jam’iyyun siyasa daban-daban, ya buga misali da yadda Kwankwaso a matsayinsa na Gwamnan Kano ya bi sahun wasu gwamnonin jihohin Sakkwato da Adamawa da Ribas wajen sauya sheƙa daga PDP zuwa APC.

Sai dai Shekarau ya bayyana cewa shugabannin riƙon kwarya na APC a wancan lokacin da suka haɗa da Bisi Akande, Muhammadu Buhari, da Bola Tinubu, sun kasa tabbatar da adalci a tsarin jam’iyyar.

“A Kano jam’iyyar ANPP ce ta kafa kashi 80 cikin 100 na jam’iyyar APC, amma saboda kasancewar shi [Kwankwaso] gwamna mai ci sai suka ware masa kashi 60 cikin 100 na shugabancin jam’iyyar, wanda muka ɗauki hakan a matsayin rashin adalci,” in ji Shekarau.

Da yake buga wani misalin, Sanata Shekarau ya ce “akwai cin fuska idan ka je sabon gidan da wasu suka gina babu gudunmawarka, ka tarar da mazauna a gidan, sai ka nemi ka yi babakere ta dole sai an ba ka ɗakin da kake so, saboda haka wannan ba abu ne mai yiwuwa ba. Shi ya sa muka ƙi goyon bayan irin wannan rashin adalci,” inji shi.

Ya ƙara bayar da misali da irin abin da ya faru a jam’iyyar PDP, yana mai cewa “a can ma Kwankwaso ba shi ne abin zargi ba, domin shugabannin jam’iyyar ne suka yanke shawara.”

A cewarsa, “ko wannan batu na rashin adalci da ya taso a jam’iyyar NNPP a yanzu, yana da nasaba ne da watsi da tsarin raba madafun iko da aka amince da shi tun farko.

“Ko a yanzu ni da Kwankwaso mukan zauna mu tattauna kan wasu batutuwa. Ba mu taɓa cewa ba za mu zauna a ƙarƙashin jam’iyya ɗaya ba. Komai yana hannun Allah.

“Shekarau 20 da suka wuce, da wani zai ce maka zan zama gwamna, da ka rantse cewa ba zai yiwu ba saboda abu da mu taɓa tsammani ba—haka shi ma ya ke a wurinsa [Kwankwaso],” in ji Shekarau.

Shekarau ya nanata cewa ƙaddarar Ubangiji ta sanya da shi da Kwankwaso da Abdullahi Umar Ganduje duk suka riƙe kujerar Gwamnan Kano “ba don babu waɗanda suka fi mu cancanta sai don haka Allah Ya riga ya rubuta.

“Akwai mutane da yawa da sun fi mu ta kowane fanni na rayuwa, amma Allah Ya zaɓe mu,” in ji Shekarau .

Aminiya ta ruwaito cewa a baya-bayan nan ana ƙoƙarin ganin an haɗa kan manyan ‘yan siyasar Kano —Kwankwaso, Ganduje da Shekarau — domin ci gaban jihar.

Ko a kwanakin tsohon ɗan takarar kujerar Sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyyar APC, Alhaji Abdulsalam Abdulkarim Zaura, wanda aka fi sani da AA Zaura, ya bayyana aniyarsa ta sasanta manyan ‘yan siyasar jihar guda uku.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abdullahi Umar Ganduje Jihar Kano Malam Ibrahim Shekarau Rabi u Musa Kwankwaso da Kwankwaso a jam iyyar Shekarau ya

এছাড়াও পড়ুন:

Gobara ta ƙone shaguna 17 a tsohuwar kasuwar Gombe

Wata mummunar gobara ta ƙone shaguna sama da 17 a ɓangaren ’yan teloli da masu hada-hadar kayan abinci a tsohuwar kasuwar garin Gombe.

Gobarar, wadda ta fara da misalin ƙarfe 2:00 na dare, ta jefa ’yan kasuwa cikin jimamin asarar dukiya mai tarin yawa da aka kiyasta ta kai miliyoyin naira.

Mijina bai hana ni waƙa ba sai dai… – Fa’iza Badawa Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata

Wasu da lamarin ya faru a kan idonsu, sun bayyana cewa gobarar ta bazu cikin sauri, inda ta riƙa laƙume kaya da kadarori kafin ’yan kwana-kwana su iso wurin.

Ko da yake ba a tabbatar da musabbabin tashin gobarar ba, amma wasu ’yan kasuwar na zargin cewa matsalar wutar lantarki ce ta haddasa ta.

Wani daga cikin ’yan kasuwar da lamarin ya shafa, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana bakin cikinsa da cewa, “Mun rasa komai.

“Mutanenmu da dama sun saro kaya a kwanan nan, amma yanzu duk sun ƙone. Wannan babban kalubale ne a gare mu.”

Wakilinmu ya ruwaito cewa jami’an hukumar kashe gobara ta Jihar Gombe tare da gudunmawar wasu mazauna ne suka taimaka wajen hana gobarar bazuwa zuwa wasu sassan kasuwar.

Sai dai, kafin a kashe gobarar gaba ɗaya, tuni ta riga ta yi mummunar ɓarna.

Har yanzu mahukunta ba su fitar da wata sanarwa game da lamarin ba, sai dai shugabannin ’yan kasuwa suna kira ga gwamnati da ta taimaka wa ’yan kasuwar da abin ya shafa.

Sun kuma yi kira da a ɗauki tsauraran matakan daƙile gobara don hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Wannan gobarar ta shiga jerin gobarar da suka auku a kasuwannin Gombe a cikin ’yan shekarun nan, lamarin da ya jaddada muhimmancin samar da ingantattun matakan daƙile aukuwarta a wuraren kasuwanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ta Amince Da Gazawarta Wajen Hana Harin Hamas
  • Yemen Ta Gargadi HKI Kan Ci Gaba Da Hana Shigar Kayakin Agaji Zuwa Yankin Gaza
  • Gobara ta ƙone shaguna 17 a tsohuwar kasuwar Gombe
  • Mijina bai hana ni waƙa ba sai dai… – Fa’iza Badawa
  • Jami’an tsaro sun hana jama’a kwasar mai bayan hatsarin tanka a Taraba
  • NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ Ba
  • Masar : Za’a Gabatar Da Shirin Baiwa Falasdinawa Yancin Zama A Kasarsu
  • MDD, Ta Damu Da Matakin Isra’ila Na Hana Shigar Da Kayan Agaji Gaza
  • Hamas: Babu Wani Karin Tattaunawa Da HKI, A Aiwatar Da Yarjeniyar Kamar Yadda Take