Bayan haka, ƙungiyoyi da jama’a da dama sun buƙaci a yi bincike kan lamarin, wanda ya kai ga Majalisar Dattawa ta buƙaci Sanata Natasha ta bayyana kanta da kuma gabatar da ƙorafi a hukumance.

Sanata Natasha Ta Gabatar Da Ƙorafinta

A ranar Laraba ta gabatar da ƙorafin, Sanata Natasha ta isa majalisar ne tare da mai gidanta, sannan ta yi magana kai-tsaye ga Shugaban Majalisar.

Ta ce: “Ina gabatar da ƙorafi kan Shugaban Majalisar Dattawa, mai girma Sanata Godswill Akpabio, bisa cin zarafi, tursasawa da ƙoƙarin daƙile min aikina a matsayin ƴar majalisa.”

Daga nan, ta sauka daga kujerarta zuwa gaban Akpabio, inda ta rusuna tare da miƙa takardun ƙorafinta.

Martanin Akpabio

Sanata Akpabio ya karɓi ƙorafin Natasha, amma ya yi watsi da zarge-zargen da ta ke masa.

“Na miƙa wannan ƙorafi ga kwamitin ladabtarwa don yin nazari. Amma ina so na fayyace cewa ba ni da wata alaƙa da zargin cin zarafi da aka yi min.”

Ya ci gaba da cewa bai taɓa cin zarafin wata mace ba, yana mai bayyana cewa mahaifiyarsa ta koya masa mutunta mata.

Ya kuma ƙara da cewa yana da ‘ya’ya mata huɗu, don haka ba zai taɓa aikata abin da ake zarginsa da shi ba.

Ƴan Majalisa Ba Su Goyi Bayan Natasha Ba

Duk da cewa Sanata Natasha ta gabatar da ƙorafinta, kusan dukkanin ƴan majalisar da suka yi tsokaci ba su goyi bayan ta ba.

Hatta Sanatoci mata ƴan uwanta ba su mara mata baya.

Wasu sanatocin sun ce irin wannan ƙorafi bai dace a gabatar da shi a majalisa ba, yayin da wasu suka buƙaci a yi ganawar sirri kan batun.

Sai dai Akpabio ya ce hakan ba zai yiwu ba, domin akwai wakilai daga Birtaniya da suka halarci zaman majalisar domin nazarin yadda al’amura ke gudana.

Tuni lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a cikin majalisa da wajenta,

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Cin Zarafi Majalisar Dattawa Zargi gabatar da ƙorafi a gabatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙarin ’yan Najeriya za su fuskanci talauci nan da 2027 — Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi hasashen cewa talauci a Najeriya zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari a cikin shekaru biyar masu zuwa, ciki har da shekarar zaɓe ta 2027.

Wannan hasashe yana ƙunshe ne a cikin rahoton Bankin wanda aka fitar a lokacin taron bazara na Bankin Duniya da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da ake yi a birnin Washington, D.C., a ƙasar Amurka.

Rahoton ya jaddada cewa duk da wasu nasarorin da aka samu a harkokin tattalin arziki a kwanakin baya, musamman a ɓangaren da ba na man fetur ba a cikin rubu’i na ƙarshe na shekarar 2024, matsalolin da suka shafi dogaro da albarkatun ƙasa da kuma raunin ƙasa na iya kawo cikas ga ci gaba.

A cewar Bankin Duniya, Najeriya, tare da wasu ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni a yankin kudu da Sahara, za su fuskanci ƙaruwar talauci —saɓanin ƙasashen marasa arzikin albarkatu, waɗanda ake tsammanin za su samu raguwar talauci cikin sauri.

’Yan bindiga sun kashe ango, sun sace amarya a Nasarawa NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani

Rahoton ya bayyana cewa, “Ana hasashen talauci zai ƙaru da kashi 3.6 cikin ɗari tsakanin 2022 zuwa 2027a ƙasashe masu arzikin albarkatu da masu rauni—ciki har da manyan masu tattalin arziƙo kamar Najeriya da Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango.”

A halin da ake ciki, Sanatan da ke wakiltar Ondo ta Kudu, Jimoh Ibrahim, ya yi kira ga ƙasashen a Afirka, Bankin Duniya, da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) da su ba da fifiko ga amfani da bayanai don ci gaban Afirka.

Da yake magana a yayin taron bazara na IMF/Bankin Duniya a Washington, D.C., Amurka, Sanata Jimoh Ibrahim ya jaddada muhimmancin bayanai a ci gaban tattalin arziki da siyasa.

Ya ce, “Idan babu bayanai ba, babu wanda zai iya rage aikata laifuka yadda ya kamata ko kuma gudanar da gwamnatin da ke da nufin cimma nasarar rage talauci.”

Ya ƙara da cewa, “Bayanai kan yawan jama’a da cikakkun bayanai na mutane sun nuna cewa ya kamata ’yan ƙasa su mallaki fasfo na tantancewa domin tattara muhimman bayanai game da su wane ne su da kuma abin da suke yi.”

Sanatan ya yi gargadi ga IMF game da yin hasashe ba tare da ingantattun bayanai ba, yana mai cewa irin waɗannan hanyoyin ba su da inganci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina Ta Sauya Masu Yi Wa Alhazai Hidima A Saudiyya
  • Zaɓen 2027: ’Yan Najeriya za su yanke wa Tinubu hukunci — PDP
  • Ƙarin ’yan Najeriya za su fuskanci talauci nan da 2027 — Bankin Duniya
  •  Ministan Tsaron Pakistan Ya Yi Wa Pakistan Barazanar Kai Mata Hari Mai  Tsanani
  • An kama wasu mata na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 47 A Birnin El-Fasher Fadar Mulkin Darfur Ta Arewa
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Mahmuda: Sabuwar ƙungiyar ’yan ta’adda ta ɓulla a Nijeriya
  • ‘Yan majalisar dokokin Aljeriya sun yi kira da a haramta daidaita alaka da Isra’ila