HausaTv:
2025-04-05@04:46:12 GMT

Trump Ya Yi Barazanar Korar Daliban Da Ke Goyon Bayan Falasdinawa

Published: 5th, March 2025 GMT

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar rage kudaden da gwamnatin tarayya ke ba wa kwalejoji da jami’o’in da ke ba da izinin ” zanga-zangar goyan bayan Falasdinawa tare da hukunta daliban da suka shiga irin wannan zanga zanga.

Trump ya yi wannan gargadin ne a wani sako da ya wallafa a dandalinsa na sada zumunta bayan da masu zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa suka taru a harabar jami’ar Columbia da ke New York.

Shugaban na Amurka ya kara da cewa “za a daure masu tayar da hankali” ko dai a daure su ko kuma a tura su dindindin zuwa kasashensu na asali.”

Ko da yake bai ambaci musamman zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a cikin sakon nasa ba, amma a baya Trump ya yi barazanar korar duk daliban da suka shiga zanga-zangar adawa da kisan kiyashin da Isra’ila ke yi wa Falasdinawa a zirin Gaza.

A karshen watan Janairu, Trump ya rattaba hannu kan wata doka da ta bukaci gwamnati ta kori daliban kasashen waje da suka shiga zanga-zangar goyon bayan Falasdinu.

Ya yi zargin cewa zanga-zangar da aka yi a harabar jami’ar ta haifar da “kyama, barna da kuma cin zarafi a kan ‘yan kasarmu, musamman a makarantunmu da harabar jami’armu.”

Kungiyoyin kare hakkin bil’adama da masana shari’a sun dage cewa wannan umarni ya saba wa ‘yancin fadin albarkacin baki da kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: bayan Falasdinawa zanga zangar Trump ya yi

এছাড়াও পড়ুন:

 Falasdinawa 86 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Falasdinu ta sanar da cewa adadin wadanda su ka yi shahada a cikin sa’o’I 24 da su ka wuce, sun kai 86, yayin da wadanda su ka jikkata kuwa sun kai 287.

Asibitocin yankin na Gaza sun karbi wannan adadin na  shahidai da kuma wadanda su ka jikkata, suna karbar magani.

Ma’aikatar harkokin kiwon lafiyar ta Falasdinawa ta kara da cewa ya zuwa yanzu jumillar Falasdinawan da HKI ta kashe tun daga 7 ga watan Oktoba na 2023 zuwa yanzu sun haura dubu 50.

Bugu da kari a halin da ake ciki da akwai gawawwakin shahidai masu yawa da suke kwance a karkashin baraguzan gidajen da HKI ta rushe da mutane a cikinsu, da kuma wadanda ta kashe akan hanya a lokacin da suke tafiyar zuwa inda za su sami mafaka.

Yankunan da HKI ta tsananta kai wa hare-hare a yau sun hada Khan-Yunus da kuma Arewacin Rafah.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Falasdinawa 86 Ne Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Da Su Ka Gabata
  • Iran ta yi kira ga kungiyar Shanghai ta yi Allah wadai da barazanar Trump
  • Turji ya kusa komawa ga mahallici –  Sojoji
  • Burundi ta zargin Rwanda da yunkurin kai mata hari
  • Matafiya sun maƙale bayan ruftawar gada a Taraba
  • Uromi: Matar Mamaci Ta Haihu Bayan Rasuwar Mijinta, Ta Nemi Taimako
  • Janar Tsiga Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Bayan Shafe Kwanaki 56 A Hannun ‘Yan Bindiga 
  • Janar Tsiga ya kuɓuta bayan shafe kwana 56 a hannun ’yan bindiga
  • Isra’ila na karbe yankuna a zirin Gaza
  • ‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga, Sun Ceto Ɗalibai 2 A Nasarawa