Wata koto a nan Tehran ta ci gwamnatin Amurka taran dalar Amurka biliyon $12.6 saboda hana wadanda suke fama da cutar ‘Talamessia” a kasar.

Tashar talabijin ta Presstv  a nan Tehran ta ce a shekara ta 2018 ne gwamnatin kasar Amurka ta fice daga yarjeniyar JCPOA ta shirin Nukliyar kasar sannan ta dorawa kasar Iran takunkuman tattalin arziki mafi muni, wanda ya hada da magungunan cutar Talassemia.

Labarin ya kara da cewa Kotu mai lamba 55 wanda yake kula da kararraki na kasa da kasa a jiya Laraba ta yanke hukun kan wasu jami’an gwamnatin Amurka wadanda suke da hannun kasi tsaye na wajen dorawa kasar takunkuman tattalin arziki har da magungun wannan cutar.

Kafin haka dai masu fama da wannan cutar  thalassemia 438 ne suka shigar da kara kan mutane 17 na gwamnatin Amurka wadanda suke da hannu wajen aiwatar da takunkuman tattalin arziki na magunguna a Amurka.

Kotun ta yanke hukuncin tarar ne a kan wadanda Jami’an gwamnatin Amurka, wadanda suka hada da wadanda cutar ta gurgunta, ko ta yi masu wata illa. Ko barna ga masu mafa da cutar. Magungunar cutar Thalassemia masu kyau dai ana samunsu a kasar Amurka ne. Rashin samunsu ya tilastawa wasu amfani da jabun magani daga wasu kasashen wanda hakan ya kara yawan kudaden da suke kashewa cutar.. Takunkuman tattalin arzikin sun gurgunta ko sun jawo mutuwar mutane da dama a kasar Iran don haka wannan tarar ta dace da irin wannan laifin

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: gwamnatin Amurka

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB

Ya buƙaci jama’a da su ci gaba da tallafa wa jami’an tsafta domin tabbatar da tsaftar muhalli a jihar.

Aikin tsaftar muhalli na wata-wata, wanda ake yi a ƙarshen kowane wata, ana dakatar da zirga-zirgar ababen hawa na wasu awanni domin tsaftace muhalli a faɗin Kano.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta Bayyana cewa: TattaunawarMuscat Wata Dama Ce Ta Samun Zaman Lafiya Kan Batutuwan Masu Sarkakiya
  • An Gano Naira Miliyan 27.8 Da Suke Zirarewa A Albashin Kano
  • Rasha Ta Fara Aika Isakar Gas Zuwa Kasar  Iran Ta Azarbaijan Don Sayarwa A Kasuwannin Duniya
  • Gidauniyar Dangote Ta Kai Tallafin Abinci Ga Wadanda Iftila’in Gobara Ya Ritsa Da Su A Jigawa
  • Sojonin Yemen Ta Kakkabo Jiragen Yakin Amurka Wadanda Kimarsu Ya Dalar Amurka Miliyon $200 A Makonni 6
  • Zanga-zangar Lumana Wani Bangare Ne Na Mulkin Dimokuradiyya
  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shirin Tsaftar Muhalli Na Wata Wata Saboda Jarrabawar JAMB
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Gwamnatin Haramtacciyar Isra’ila Tana Azabtar Da Falasdinawa A Gidajen Kurkukunta