Aminiya:
2025-04-07@13:20:07 GMT

Sibil Difens za ta da ɗauki sabbin ma’aikata

Published: 6th, March 2025 GMT

Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) ta samu sahalewar Shugaban Ƙasa na ƙara daukar sabbin ma’aikata.

Babban Kwamandan Hukumar, Ahmed Aifi, na ya sanar da haka, a yayin ƙaddamar da Baban Ofishin Yanki na Hukumar a Ƙaramar Hukumar Bwari da ke yankin Babban Birnin Tarayya a ranar Laraba.

“Nan gaba kaɗan za mu ɗauki ’yan Najeriya masu kyawawan ɗabi’u a matsayin jami’ain Sibil Difens, kuma muna godiya ga shugaban ƙasa bisa wannan dama da ya ba hukumar,” in ji shi.

Ya bayyana cewa Hukumar ta fara shirye-shiryen ɗaukar sabbin, amma sai nan gaba za ta sanar da ranar fara ɗaukar tasu.

An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba?

Ya kuma yaba wa Majalisar Ƙaramar Hukumar Bwari bisa gina ofishin, wanda ya ce zai taimaka wajen inganta tsaro.

Olusola Odumosu, wanda shi ne Kwamandan Hukumar, ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar, John Gabata da ya samar da ofishin cikin kyakkyawan yanayi ga jami’an hukumar tsaron.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwari daukar sabbin jami ai Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Mutanen Algeriya sun bukaci a rufe ofishin jakadancin Amurka a kasarsu

Dubun-dubatar al’ummar kasar Aljeriya sun gudanar da wani gagarumin gangami da jerin a wannan Juma’a a birnin Algiers babban birnin kasar, domin yin Allawadai da laifukan yaki da Haramtacciyar Kasar Isra’ila take aikatawa a kan al’ummar yankin zirin Gaza.

Kamar yadda kungiyar Movement of Society for Peace ta yi kira, dubban  ‘yan kasar Aljeriya ne suka fito domin nuna goyon baya ga al’ummar Palasdinu a gaban hedikwatar jam’iyyar da ke unguwar  al-Mouradia, babban birnin kasar Aljeriya.

Sai dai hukumomin Aljeriya sun kewaye masu zanga-zangar don hana fadada zanga-zangar zuwa wuraren da jama’a ke taruwa.

Masu zanga-zangar sun yi ta rera taken nuna rashin amincewarsu da kisan kiyashin da “Isra’ila” ke yi a Gaza, inda suka yi Allah wadai da saka al’ummar Gaza a cikin yunwa da kuma ci gaba da aiwatar da  kashe-kashen da Isra’ila ke yi, da nufin tilasta wa al’ummar Palasdinu kauracewa gidajensu da yankunansu . Masu zanga-zangar sun kuma yi kira da a rufe ofishin jakadancin Amurka da ke Aljeriya, saboda rawar da Amurka ta take takawa wajen mara wa Isra’ila baya ga laifukan Isra’ila a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta kaddamar da sabbin hare-hare kan Yemen
  • Fulham ta doke Liverpool bayan wasa 26 a jere ba tare da rashin nasara ba
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Hamas Ta Yaba Da Ma’aikaciyar Kamfanin Microsoft Wacce Ta Fallasa Yadda Kamfanin Yake Taimakawa HKI
  • Rasha za ta bude ofishin jakadanci a Nijar nan ba da jimawa ba
  • Euro-Med : Laifukan da Isra’ila ta aikata a Gaza sun zarce na Daesh
  • Boko Haram haram ta kashe ɗan sanda a sabon hari a Borno
  • Mutanen Algeriya sun bukaci a rufe ofishin jakadancin Amurka a kasarsu
  • Shugaba Tinubu Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Dr Idris Dutsen Tanshi
  • ’Yan sanda ku yi amfani da iko cikin adalci — CP Wakili