Aminiya:
2025-03-06@13:25:17 GMT

Hukumar Sibil Difens za ta ɗauki sabbin jami’ai

Published: 6th, March 2025 GMT

Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) ta samu sahalewar Shugaban Ƙasa na ƙara daukar sabbin ma’aikata.

Babban Kwamandan Hukumar, Ahmed Aifi, na ya sanar da haka, a yayin ƙaddamar da Baban Ofishin Yanki na Hukumar a Ƙaramar Hukumar Bwari da ke yankin Babban Birnin Tarayya a ranar Laraba.

“Nan gaba kaɗan za mu ɗauki ’yan Najeriya masu kyawawan ɗabi’u a matsayin jami’ai a Sibil Difens, kuma muna godiya ga shugaban ƙasa bisa wannan dama da ya ba hukumar,” in ji shi.

Ya bayyana cewa Hukumar ta fara shirye-shiryen ɗaukar sabbin, amma sai nan gaba za ta sanar da ranar fara ɗaukar tasu.

An yanke wa masu fyaɗe 3 hukuncin dandanƙewa da rataya a Kaduna An kama korarren jami’in tsaro da ke sayar wa ’yan ta’adda makamai NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Su Ga Ragi A Farashin Man Fetur Ba?

Ya kuma yaba wa Majalisar Ƙaramar Hukumar Bwari bisa gina ofishin, wanda ya ce zai taimaka wajen inganta tsaro.

Olusola Odumosu, wanda shi ne Kwamandan Hukumar, ya yaba wa shugaban ƙaramar hukumar, John Gabata da ya samar da ofishin cikin kyakkyawan yanayi ga jami’an hukumar tsaron.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwari daukar sabbin jami ai Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

A Kasar Sudan Ta Kudu  Jami’an Tsaro Sun Killace Gidan Mataimakin Shugaban Kasa

Kamfanin dillancin Labarun “Resuters” ya nakalto cewa jami’an tsaro sun killace gidan mataimakin shugaban kasa da wasu manyan jami’an soja da fararen hula.

Baya ga mataimakin shugaban kasa  Riek Machar da sojoji su ka yi wa daurin talala a cikin gidansa, an kuma  kama mataimakin hafsan hafsoshin sojan kasar Jamar Gabriel Doup Lam, sai kuma ministan man fetur Pout Kang Chol, haka nan kuma iyalansa da masu gadinsa.

Har ila yau a jiya Laraba an ga jami’an tsaro masu yawa sun killace ofishin mataimakin shugaban kasar, sai dai kuma wata majiyar ta ce, an gan shi ya isa wajen aikin nashi da safiyar jiya Laraba.

Wadannan matakan na tsaro dai sun biyo bayan fada mai tsanani da aka yi ne  a tsakanin sojojin gwamnatin da kuma mayakan kabilar Nuwairah wacce mataimakin babban hafsan hafsoshin sojan kasar ya fito daga cikinta.

Gwamnatin shugaba Silva Kir tana tuhumar janar Doup Lam da cewa yana da hannu a tawayen ‘yan kalbilar tashi.

An sami asrar rayuka masu yawa a wannan fadan a tsakanin bangarorin biyu.

Shugaba Silva ya yi alkawalin cewa kasar ba za ta sake komawa cikin yaki ba.

A 2013 ne dai kasar ta Sudan Ta Kudu ta tsunduma cikin yakin basasa wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutanen da sun kai 400,000 da kuma mayar da mutane miliyan 2.5 zama ‘yan gudun hijira.

Jumillar mutanen kasar da sun kai miliyan 11 suna fafutukar samun abinci da kuma ruwan sha mai tsafta. Sai dai daga baya na yi sulhu a tsakanin bangarorin biyu na shugaba Silva Kir da kuma mataimakinsa Riek Machar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • A Kasar Sudan Ta Kudu  Jami’an Tsaro Sun Killace Gidan Mataimakin Shugaban Kasa
  • Sibil Difens za ta da ɗauki sabbin ma’aikata
  • Majalisar Kano ta yi wa dokar hukumar tace fina-finai gyaran fuska
  • Hukumar Leken Asirin Isra’ila Ta Amince Da Gazawarta Wajen Hana Harin Hamas
  • Majalisar Zartarwa Ta Tarayyar Najeriya Ta Amince Da Kirkirar Sabbin Jami’oi 11
  • ‘Yan Fashi Da Makami Sun Kashe Tsohon Babban Kwanturolan Hukumar NIS A Abuja 
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD Ta Ce Sauye-Sauyen Da Ke Faruwa A Amurka Zai Shafi Al-Amura Da Dama A Majalisar
  • Jami’an tsaro sun hana jama’a kwasar mai bayan hatsarin tanka a Taraba
  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Gargadi Malaman Da Ba Sa Zuwa Aiki