Najeriya Ta Shirya Aiwatarda Yarjejeniyar Fahimta Tsakanin NTA, FRCN Da China Media Group
Published: 6th, March 2025 GMT
Ministan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya jaddada kudurin Najeriya na aiwatar da cikakken yarjejeniyar biyu da aka kulla tsakanin China Media Group da manyan gidajen watsa labarai na gwamnati a Najeriya – Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) da Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN) a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka gudanar a Beijing.
Ministan ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi Jakadan Sin a Najeriya, Mista Yu Dunhai, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a ofishinsa a yau alhamis. Ya ce, wadannan yarjejeniyoyi sun ƙudiri aniyar ƙarfafa haɗin gwiwa a fannin watsa labarai da sadarwa, domin inganta dangantakar Najeriya da Sin.
Ya bayyana cewa yarjejeniyoyin sun shafi musayar bayanai da fasahar zamani, wanda hakan zai inganta ƙwarewar gidajen watsa labaran Najeriya tare da ɗaukaka su zuwa matakin da ya dace da kyawawan ƙa’idojin duniya.
“Najeriya da Sin a matakin hulɗar diflomasiyya suna da ƙawance mai ƙarfi matuka. Wannan ya haifar da sanya hannu kan yarjejeniyar fahimta guda 10 a Beijing, kuma guda biyu daga cikinsu suna da nasaba da wannan ma’aikata. Hukumar Talabijin ta Najeriya (NTA) ita ce cibiyar talabijin mafi girma a duk faɗin Afirka, tana da tashoshi sama da 100 da ke rufe dukkan yankuna tare da isa ga mutane sama da miliyan 200. Yana da matuƙar muhimmanci, kuma abin da NTA ke son cimmawa ta hanyar wannan haɗin gwiwa da Sin shi ne musayar labarai, fasaha, da bayanai wanda zai amfanar da ƙasashen biyu. Haka kuma, muna da irin wannan yarjejeniya da ɗaya daga cikin manyan gidajen rediyo a Afirka, wato Hukumar Rediyon Tarayyar Najeriya (FRCN). Wadannan yarjejeniyoyi sun riga sun kammala, kuma Najeriya tana da niyyar cika nata ɓangaren,” in ji shi.
Ministan ya ce, bayar da sahihin bayani da labarai na gaskiya zai ƙara ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashe, don haka ya nemi haɗin gwiwa da Sin wajen yaƙi da labaran ƙarya, ɓata bayani da yada bayanai na bogi.
“Yada labaran ƙarya ƙalubale ne ga duniya baki ɗaya. Mun san cewa Sin tana ɗaukar wannan batu da muhimmanci sosai, haka kuma mu ma a Najeriya muna ɗaukar hakan da muhimmanci. Ba matsala ba ce da ke shafar Najeriya da Sin kaɗai; matsala ce ta duniya baki ɗaya, kuma muna son yin aiki tare da Sin don yaƙi da labaran ƙarya tare da inganta watsa labarai masu amfani da za su taimaka wajen bunƙasa al’umma,” in ji shi.
Idris ya bayyana wa Jakadan cewa, Najeriya na da ‘yancin watsa labarai a matsayin wani muhimmin bangare na manufofin gwamnatin Tinubu don ƙarfafa dimokuradiyya ta hanyar bayar da ingantattun bayanai.
“Kafafen watsa labarai a nan suna da ’yanci sosai. Tabbas, akwai wasu matsaloli a lokaci zuwa lokaci, wanda koyaushe muna aiki a kansu don ingantawa. Najeriya na da babbar ’yancin watsa labarai, kuma muna so mu ci gaba da hakan,” in ji shi.
Ministan ya kuma bukaci kamfanonin Sin su yi amfani da sauye-sauyen da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa domin zuba jari a tattalin arzikin Najeriya.
A nasa jawabin, Jakada Dunhai ya ce a matsayinsa na sabon jakadan Sin a Najeriya, zai yi duk mai yiwuwa don ƙara ƙarfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.
Ya nuna goyon bayansa ga shirin “Renewed Hope Agenda” na Shugaba Tinubu, wanda ke da nufin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa don samar da ci gaba mai dorewa.
“A matsayina na sabon jakada, ina ganin kaina a matsayin mai sa’a saboda na zo ne a lokacin da Najeriya ke karkashin jagorancin Shugaba Tinubu, wanda ke da niyyar gina ƙasa mai ƙarfi. Haka nan, a karkashin jagorancin Shugaba Xi Jinping, Sin tana kan tafarkin sabunta ƙasa ta hanyar tsarin zamani na Sin,” in ji shi.
Jakadan ya tunatar da cewa a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a Beijing, Shugabannin kasashen biyu, Xi Jinping da Tinubu, sun amince da ɗaukaka dangantakar kasashen su zuwa babbar kawance ta fuskar diflomasiyya, wanda hakan zai buɗe sabon babi a dangantakar su.
Ya ce yana sa ran ganin yadda za a aiwatar da yarjejeniyoyin fahimta da aka kulla tsakanin NTA, FRCN da China Media Group, domin kafafen yada labarai suna da muhimmiyar rawa da suke takawa wajen gina al’umma.
Jakadan ya bayyana jin daɗinsa cewa kafafen watsa labarai a Najeriya suna daidaito, gaskiya da adalci a labaran da suke watsawa, domin suna ƙoƙarin gabatar da cikakken bayani kan abubuwan da ke faruwa ga ‘yan Najeriya.
A bangaren zuba jari, Jakadan ya ce Shugaba Xi Jinping ya alkawarta dala biliyan 50 domin zuba jari a Afirka a cikin shekaru uku masu zuwa, a matsayin ci gaba ga yarjejeniyoyin fahimta guda goma da aka rattaba hannu a taron hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka da aka yi a baya-bayan nan.
Cov/Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Aiwatarda Najeriya Shirya Yarjejeniyar
এছাড়াও পড়ুন:
Sharhin Bayan Labarai: Shin Kissan Mutanen Gaza Gaba Daya
Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana a kan ‘wani makircin da kasar faransa ta kullawa falasdinawa a gaza’ don su amfana da kwararrunsu’ wanda ni tahir amin zan karanta.
///… Shugaba kungiyar kare hakkin bil’adama masi suna [the Euro-Mediterranean Human Rights Monitor] ta fallasa wani shiri tsakanin gwamnatin kasar faransa da HKI na fitar da kwararru da kuma masana falasdinawa da suka rage a Gaza, zuwa wajen yankin, kafin HKI ta fa wani gagarumin kissan kiyashi a yankin kashe falasdinawa da suka rage a yankin.
Kamfanin dillancin labaran Parstoday na kasar Iran ya nakalto Ramy Abdu shugaban kungiyar na fadar haka, ta kuma kara da cewa, offishin jakadancin kasar Faransa da ke birnin Qudus da aka mamaye, yana aiki tare da HKI don zakulo masana da kwararru a fannonin ilmi daban daban da ke tsare a cikin zirin gaza, zuwa wajen yankin saboda amfani da su don amfanin kansu.
Rahoton ya kara da cewa, wadanda zasu fitar daga yankin na Gaza, sun hada da dukkan masu digiri na uku wato PHD, likitoci, inginiyoyi, masanan tarihi da kuma wadanda suke da korewa a abubuwan al-adu da kayakin tarihi .
Kamfanin dillancin labaran Parstoday a kara da cewa wannan shi ne wannan gagarumin aiki mikirce ne tsakanin Faransa da sojojin HKI na korar Falasdinawa daga Zirin gaza. Wannan shirin, inji Ramy Abdu ya sabawa dokokin kasa da kasa, kuma kasar faransa ta fada cikin wannan laifin wanda ake iya gurfanar da kasar da ta aikata haka a gaban kuliya.
Abdu ta kara da cewa abinda HKI ta kasa samu tare da amfani da makami tana son ta yi amfani da kungiyoyin kare hakkin bil’adama don cimma wanna manufar.
Kafar yada labarai da kasar Burtaniya mai suna ‘Middle East Eye’ HKI ta fara wani shiri na musamman, mai matakai 5 don tabbatar da ba wani bafalasdine da ya rage a Gaza, wanda kuma zai bata damar kafa kasar “yahudawa zalla’ a kan kasar Falasdinu.
Yahudawan sun sha nanata manufarsu ta ganin dukkan falasdinawa sun fice daga Gaza da kuma yankin yamma da kogin Jordan tun bayan an fara yakin 7 ga watan Octpba shekara ta 2023.
Jaridar ta kara da cewa gwamnatin HKI ta fara aiwatar da wannan shirin, yana da matakai 5, kuma sun hada da, saka Falasdinawan cikin yunwa, rage yawan falasdinawa a gazar ta hanyar kashe su matukar iyawarsu, da lalata tsarin kiwon lafiya, ta yadda dan karamin cuta zata kashesu, maida gaza wurin da ba wanda zai ita rayuwa cikinsa, sannan daga karshe anfani da dokokin kasa da kasa na maida gaza bangare na HKI bayan sun kammala kashe sauran falasdinawa a yankin.
Wannan ya nuna cewa zasu kashe falasdinawa kimani miliyon 2 a cikin karamin. Don haka a wannan tsarin suna ganin a mataki na 5 sun kammala kashe dukkan falasdinawa a gaza.
Jaridar ta kammala da cewa idan wannan shirin bai yi aiki ba suna da wani tsari wanda zai kasu ga shafe dukkan Falasdinawa a gaza. A cikin watan Jenerun wannan shekara ne shugaban kasar Amurka Donal trump ya bayyana wannan ra’ayin. Sai dai wannan ba ra’ayinsa na karan kansa ba, ra’ayi ne na yahudawan na samar da kasar yahudawa zalla tun asali.