Gwamnatin jihar Kebbi, ta kaddamar da rabon kayayyakin noman rani da kayan abinci na watan Ramadan ga manoma da al’ummar jihar, inda ta umurci jami’an tsaro da su kama duk wanda aka samu yana sayar da kayan abinci da na aikin noma.

A jawabinsa yayin kaddamar da rabon, gwamnan jihar, Kwamared Nasir Idris ya bayyana cewa, matsakaitan manoma 200,000 a fadin kananan hukumomin jihar 21 ne za su ci gajiyar shirin.

Gwamnan ya bayyana cewa, samar da kayan aikin gona ga manoma zai taimaka wajen bunkasa samar da abinci a jihar.

Ya yi kira ga shugabannin addini da na al’umma da kuma jami’an gwamnati da ke da alhakin rabon kayayyakin, da su tabbatar da an yi adalcin wajen  rabon kayayyakin.

Ministan noma da samar da abinci, Abubakar Kyari, ya ce shugaba Bola Tinubu, yana bakin kokarinsa wajen inganta harkar noma, ta hanyar karfafa gwiwar kowane bangare na al’umma da su ba da muhimmanci ga shirin noma na gwamnati.

Ya ce, rabon kayayyakin amfanin gona ga manoma a jihar Kebbi shi ne don bunkasa ayyukan noman rani a shekarar 2025, domin kara yawan kayan abinci a jihar da kuma dakile matsalar karancin abinci.

Kwamishinan noma na jihar Alhaji Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen inganta kayan noma da kuma dakile matsalar karancin abinci.

Ya ce, matakin da gwamnati ta dauka shi ne rage wa manoma wahalhalu a lokacin noman rani tare da rage radadin da talakawa ke fuskanta a cikin watan Ramadan.

Kayayyakin da aka bayar sun hada da injinan wutar lantarki guda 3000, da famfo mai amfani da hasken rana guda 10,000, da famfunan ruwa na LPG guda 5000, da injin feshin maganin kwari guda 10,000 da dai sauransu.

Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Noman Rani rabon kayayyakin

এছাড়াও পড়ুন:

Lakurawa sun kashe ’yan sa-kai 13 a Kebbi

Ana fargabar cewa kimanin ’yan sa-kai 13 ne suka rasa rayukansu a wasu hare-hare da wasu ’yan bindiga da ake zargin mayaƙan Lakurawa ne suka kai Jihar Kebbi a jiya Lahadi.

Lamarin ya faru ne a yankin Morai na Ƙaramar Hukumar Augie — ɗaya daga cikin yankunan da ake cewa mayaƙan Lakurawa na da sansani.

HOTUNA: Zanga-zangar adawa da gwamnatin Tinubu ta ɓarke a Abuja da Legas Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC

Wani mazauni, Malam Ibrahim Augue, ya ce maharan sun kashe mutum shida ne, suka kwashe shanu, sai ’yan sa-kai suka bi su.

“A nan suka yi wa ’yan sa-kan kwanton ɓauna, suka buɗe musu wuta, inda suka kashe guda 13 daga cikinsu.”

Ƙoƙarin da Aminiya ta yi domin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi, CSP Nafiu Abubakar ya ci tura har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lakurawa sun kashe ’yan sa-kai 13 a Kebbi
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Rika Bayar Da Maganin Hawan Jini Da Siga Kyauta
  • ACF Ta Bukaci Gwamnatin Najeriya Da Ta Kawo Karshe Tashe-Tashen Hankula Filato
  • ACF ta nemi Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen kisan jama’a a Filato
  • Gwamnatin Yobe Ta Ƙaryata Rahoton Bayyanar Boko Haram A Babban Birnin Jihar
  • Rashin ɗa’a: Gwamnatin Borno ta gargaɗi masu amfani da shafukan sada zumunta
  • Gwamnatin Kasar Sin Ta Caccaki Matakin Kakaba Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Da Amurka Ta Dauka, Ta Kuma Sha Alwashin Kare Moriyarta
  • Rashin tsaro a Filato ya wuce rikicin manoma da makiyaya – Muftwang
  • Ɗalibai za su koma makaranta ranar Lahadi da Litinin – Gwamnatin Kano
  • Nau’in Abinci Biyar Da Ke Lalata Hanta