Karin Kudin Lantarki Da Na Kira: Kungiyar Kwadago Ta Yi Barazanar Shirya Zanga-zanga A Fadin Nijeriya
Published: 7th, March 2025 GMT
Kungiyar ta yi tir da tsarin da hukumar kulawa wutar lantarki ta yi,wanda take neman ta ba masu amfani da wuta, nau’i- nau’in da suke ko ta kai su,ba domin komai ba don wata magana ta kara bunkasa samun wutar lantarki fiye da irin halin da ake ciki yanzu.
Kamar dai yadda kungiyar tace tsarin Hukumar wani kokari ne na karin kudin wutar lantarki na sauyawa masu amfani da wuta daga tsarin da suka saba amfani da shi mai sauki zuwa ga wanda zai kasance wanda yake mai tsada.
A sanarwar da aka fitar Shugaban kungiyar da Sakatarenta Kwamrade Joe Ajaero Komrade Emmanuel Ugboaja wadda ta ce tsarin da ake shirin yi tamkar “yin laifi ne ga tattalin arzikin kasa.”
Kungiyar NLC ta ga laifin ita hukumar NERC da ma’aikatar wutar lantarki da shirin gallazawa ‘yan Nijeriya wadanda suke rayuwa ta hannu baka- hannu kwarya.
Bugu da kari kungiyar ta kara da cewa muddin aka yi wani karin kudin wutar lantarki dana kira, hakan zai sa Talakawa sun yi zanga- zanga ta kasa baki daya. Domin kuwa ma’aikata da Talakawa ba za su iya hakurin irin tsaren tsaren takura na gwamnati ba.
Ga dai yadda sanarwar take: “Kwamitin zartarwa na kungiyar kwadago ya yanke shawarar daukar mataki idan aka kasa amfani matsayar da aka cimmawa ranar 1 ga Maris 2025, ba ayi hakan ba, ba tare da bata lokaci ba an sai kwamitin zartarwa na kasa da aka dorawa alhakin daukar mataki kamar dai lamarin yake abin yake a ranar10 ga Fabrairu 2025.
“Kan shirin komawa tsarin karin kudin wutar lantarkin, majalisar zartarwar kungiyar kwadago ta yi watsi da duk wani shirin da Hukumar (NERC), yadda ake neman tursasawa masu amfani da tsarin (B) su koma tsarin (A) a karkashin wani tsarin wayo da ake kiran shi domin a kara bunkasa samar da wutar lantarki, bayan kuwa maganar gaskiya ana shiri ne na gallazawa masu amfani da wutar lantarki.
“Tsarin shirin ma’aikatar wutar lantarki ba wani abu bane illa kamar kokarin da ake yi ne na gallazawa da takurawa Talakawa wadanda suke kokarin tafiyar da rayuwarsu cikin halin kunci.”
Daga karshe kwamitin zartarwa na kungiyar kwadago koda wane lokaci cikin shirin shi yake na kare al’umma daga duk wata irin takurawa, nuna fifiko,don haka ta yi kira ga dukkan kungiyoyin da suke karkashinta, da masu da’awar ci gaba, su zama a cikin shirin kota-kwana, na shiga zanga-zanga ko nuna rashin amincewa da duk wani tsari na kuntatawa na manufofi ko tsare-tsare masu takurawa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Karin Kudin Wuta Kungiyar Kwadago Lantarki wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Shin Manchester United Za Ta Iya Lashe Kofin Europa League?
Manchester United ta kai zagayen kusa da karshe ne bayan doke Olympic Lyon ta Faransa da 5-4, bayan an yi canjaras da 2-2 a wasan farko da aka buga a Faransa. Kenan United ta yi nasara da 7-6 jimilla. Yanzu United za ta fafata wasan gab da na karshe ne da kungiyar Athletic Bilbao a ranar 21 ga watan Mayu.
Kungiyar ta Bilbao ta kai wasan karshe a gasar Europa sau biyu, na karshen a shekarar 2012, lokacin da Atletico Madrid ta doke ta da ci uku da nema a Bucharest.
Shekara 13 ke nan rabon United ta hadu da Athletic Bilbao, inda kungiyar ta Sifanya ta doke United da 2-1 a gasar ta Europa a shekarar 2012. Ita kuma United wannan ne karo na biyu da za ta buga wasan gab da na karshe a gasar Europa a shekara hudu.
A wancan karon, Manchester United ta doke Roma da ci 8:5 jimilla sai dai kungiyar Billareal ta doke ta a wasan karshe a bugun fanareti bayan an tashi wasan kunnen-doki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp