Aminiya:
2025-04-27@22:07:01 GMT

Sojoji sun hallaka mai haɗa wa Boko Haram bam a Sambisa

Published: 7th, March 2025 GMT

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe mayaƙan Boko Haram tara, ciki har da ƙwararren mai haɗa wa ƙungiyar bama-bamai, Amirul Bumma a wani samame da suka kai a dajin Sambisa da ke Jihar Borno.

Majiyoyi sun bayyana cewa sojojin sun kai farmakin ne a Ƙaramar Hukumar Bama, ƙarƙashin rundunar Operation Desert Sanity 4, bayan samun bayanan sirri.

Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha Doyin Okupe: Tsohon kakakin shugaban ƙasa ya rasu

Boko Haram sun yi ƙoƙarin tsayawa da su fafata, amma sojojin sun yi nasarar fatattakar su.

Bayan kammala artabun, mayaƙan sun dawo wajen da gadajen asibiti domin kwashe waɗanda suka jikkata, wanda hakan ke nuna girman asarar da suka yi.

Daga cikin waɗanda aka kashe akwai babban jagoran Boko Haram, Amirul Bumma tare da wasu manyan kwamandoji kamar Bakura Ghana, Awari, Malam Kalli, Malam Usman Bula Kagoye, da Ibrahim Bula Abu Asma’u.

Hakazalika, sun kashe wasu biyu da ba a tantance sunansu ba.

Har ila yau, sojojin sun ƙwato muggan makamai daga hannunsu.

A wani yunƙuri na ramuwar gayya, Boko Haram sun dasa bama-bamai a hanyar da sojojin suke bi, amma dakarun sun gano nufinsu tare da cire bama-bamai.

Babban Kwamandan runduna ta 7, Manjo Janar Abubakar Haruna, ya yababwa sojojin bisa wannan gagarumar nasara, da suka samu.

Ya jaddada cewar za su ci gaba da yaƙi da ta’addanci har sai an kawo ƙarshensa a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Artabu bayanan sirri hari Mayaƙan Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Yemen Sun Sanar Da Kai Wa Cibiyar Sojan Sama Ta “Nivatim” Hari Sau Biyu A Cikin Sa’o’i 24

Sojojin na kasar Yemen sun sake kai hari akan sansanin sojan saman a “Nivatim” na HKI a karo na biyu a cikin sa’o’i 24. Majiyar sojan kasar ta Yemen ta ce wannan shi ne karo na hudu da suke kai hari akan manufofin HKI a cikin sa’o’i 24.

Kakakin sojan kasar Yemen janar Yahya Sa’ri ya fada a wata sanar wa ta tashar talabijin cewa; sojojin kasar sun kai hari da makamai masu linzami da su ka fi sauti sauri wajen kai wa sansanin na “Nivatim” hari wanda yake a cikin yankin Naqab a Falasdinu dake karkashin mamaya.

Janar Sari ya kuma kara da cewa; hare-haren da suke kai wa HKI yana a karkashin ci gaba da taya Falasdinawa fada ne da suke yi,kuma sun sami sanarar saukar makamin a inda aka harba shi.

Haka nan kuma janar Sari ya ce; sojojin na Yemen za su ci gaba da karawa kansu karfi da yardar Allah ta hanyar bunkasa makaman da suke da su domin fuskantar ‘yan sahayoniya.

A jiya Asabar ne dai sojojin na Yemen su ka sanar da cewa sun kai hare-hare biyu da jiragen sama marasa matuki akan wasu muhimman manufofi na ‘yan sahayoniya a yankin Yafa dake karkashin mamaya da kuma a yankin Asqalan dake kusa da Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  •  Nigeria: Boko Haram Ta Kashe Mutane 12 A Borno
  • Sojojin Yemen Sun Sanar Da Kai Wa Cibiyar Sojan Sama Ta “Nivatim” Hari Sau Biyu A Cikin Sa’o’i 24
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
  • Zulum Ya Nuna Damuwa Kan Yadda Boko Haram Ke Dawowa Wasu Yankuna A Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’dda 1,770 sun kama 3,070 a Arewa —Janar Musa
  • Janyewar sojoji ke ba Boko Haram damar ƙwace yankuna —Zulum
  • Zulum Ya Taya MNJTF Da Gwamnatin Alihini Bayan Harin Boko Haram A Wulgo
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani