Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadai
Published: 7th, March 2025 GMT
Ƙungiyar Shugabannin Kiristoci ta Kudancin Kaduna (SKCLA) ta yi tofin Allah tsine da kashe Rabaran Fada Sylɓester Okechukwu na Gundumar Katolika da ke Kafanchan, inda ta jingina haka ga taɓarɓarewar harkokin tsaro a yankin.
A cikin wata sanarwa da Shugaban SKCLA, Dakta Emmanuel Nuhu Kure ya fitar a ranar Jumma’a ya miƙa ta’aziyyarsu ga Gundumar Katolika ta Kafanchan, tare da yin kira ga hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa a kan lamarin.
“Wannan mummunar aiki babbar asara ce ga Coci da matuƙar tayar da hankali da damuwa game da ci gaba da kai hare-hare ga shugabannin Kiristoci a Kudancin Kaduna,” in ji Kure.
Inda ya koka da yawan kashe-kashen shugabannin addinin Kirista da suka yawaita, inda ya yi gargaɗin cewa ci gaba da kai wa malaman addini hari na iya ɗaukar wata ma’ana da ka iya rusa zaman lafiya a jihar. “Wataƙila ‘yan ta’adda masu aikata laifi ne ke aikata hakan, amma me ya sa ake kai wa ma’aikatan cocin hari su kaɗai?” inji shi.
SKCLA ta yi kira ga hukumomi da su tabbatar da anyi adalci ga malamin da aka kashe, tare da kiran mazauna yankin da su kasance masu sa ido game da abin da ya shafi tsaro sannan su riƙa sanar da hukumomi duk wani abu da ya bayyana musu.
Idan za a iya tunawa a ranar larabar da ta gabata ne wasu ‘yan bindiga su kayi sace Faston Katolika mai suna Rabaran Fada Sylɓester Okechukwu a yankin Tachira da ke ƙaramar hukumar Ƙaura ta Jihar Kaduna inda suka kashe shi ba tare da buƙatar komai ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kaura
এছাড়াও পড়ুন:
Tashin Gobara A Tashar Jirgi Ruwa Na Shahid Raja’i Da Ke Kudancin Iran Ya Lashe Rayukan Mutane A Kudancin Iran
Daruruwan mutane ne suka jikkata sakamakon fashewar wani abu mai karfi a tashar jiragen ruwa na Shahid Raja’e da ke kudancin kasar Iran
Wata babbar fashewa, wacce ba a taba jin irin ta ba, ta afku da yammacin ranar Asabar a yankin tashar jiragen ruwa na Shahid Raja’e da ke Bandar Abbas, a kudancin kasar Iran, wanda ya yi sanadiyyar jikkata daruruwan mutane a rahotonnin da ake da su a hannu har zuwa yanzu.
A cikin wani sabon rahoton da aka samu kan adadin mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar tashar jiragen ruwa ta Shahid Raja’e, kakakin hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasar ya ce: Adadin wadanda suka jikkata ya kai 516 ya zuwa yanzu.
Fashewar ta yi karfi sosai, ta yadda mazauna Bandar Abbas da Qeshm suma suka ji karar fashewar.
Daga baya an bayyana cewa lamarin ya faru ne sakamakon fashewar tankar mai a tashar ba tare da sanin wani dalili ba, kuma nan take aka aike da tawagogin ma’aikatar bada agajin gaggawa zuwa yankin.