Aminiya:
2025-04-08@20:37:46 GMT

Kotu ta yanke wa dillalan ƙwayoyi hukuncin ɗaurin shekaru 95 

Published: 8th, March 2025 GMT

Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Legas da ta Yola, da Jihar Adamawa, sun yanke wa wasu dillalan miyagun ƙwayoyi huɗu da aka kama da safarar ƙwayoyi da darajarsu ta kai Naira biliyan 4.6 hukuncin ɗaurin shekaru 95 s gidan yari.

Ɗaya daga cikinsu, Ogbuji Christian Ifeanyi, jami’an hukumar NDLEA sun kama shi a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Legas a bara, yana ƙoƙarin shigowa da hodar iblis ɗauri 817 mai nauyin kusan kilogram 20, wadda kuɗinta ya kai biliyan 46.

Tinubu ya bai wa Farfesa Jega muƙami a gwamnatinsa PDP ta soki dakatar da Natasha, ta nemi a binciki Akpabio

Sauran da aka kama sun haɗa da Iloduba Augustine Chinonye, Shuaibu Nuhu Isa (wanda aka fi sani da Don), da kuma Zidon Zurga.

Ko da yake, ba wannan ne karo na farko da aka kama Ogbuji ba.

A baya, an kama shi watanni 16 da suka gabata bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Hukuncin Da Kotu Ta Yanke

Baya ga hukuncin ɗaurin shekaru 95 ko tarar Naira miliyan 25, kotu ta kuma umarci a ƙwace motocin da aka yi amfani da su wajen safarar ƙwayoyin.

A cikin wata sanarwa, mai magana da yawun hukumar NDLEA, Femi Babafemi, ya ce shugaban hukumar, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), ya yaba da hukuncin kotu da kuma ƙoƙarin jami’an NDLEA wajen kama masu safarar miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidan Yari ƙwayoyi Tara

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya

Rafael Grossi shugaban hukumar makamashin nukliya ta duniya (IAEA) ya bayyana cewa JMI bata da makamin Nukliya, sai dai tana dukkan kayan aikin da ake bukata,  da kuma fasahar kera makamin idan tana bukatar yin hakan.  

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Grossi yana fadar haka a wata hira da yayi da tashar talabijin ta Agentina a yan kwanakin da suka gabata. Ya kuma kara jaddada cewa a halin yanzu JMI bata da makamin Nukliya, sai dai tana da abinda ake kira “sinadarin Uranium da ta gasa, wanda yawansa zai iya samar da makaman nukliya har zuwa 6-ko 7, amma dai bata kera makamin ba.

Abinda tambaya a nan itace tunda hukumar ta tabbatar da cewa a halin yanzu Iran bata da makaman Nukliya me yasa Amurka take tada hankali kuma take barazana ga kasar dangane da shirin ta na makamashin Nukliya al-hali bata da shi?

Grossi ya bayyana cewa al-amuran siyasa da kuma takurawa kasar da kasashen yamma suke yi shi ne yake ruruta rikicin da ke faruwa tsakanin Iran da kasashen yamma. Shugaban ya tabbatar da cewa gwamnatin JMI tana bada hadin kai ga masu binciken hukumar wadanda suke gudanar da bincike a dukkan cibiyoyin makamashin nukliya na kasar ta Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Satar Mota A Bauchi
  • Kotu ta daure ango wata 6 saboda likin kudi a bikinsa
  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Ci Gaba Da Gudanar Da Taron Bita Ga Alhazai
  • Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu
  • Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina
  • NAJERIYA A YAU: Mene ne Tasirin Shirin NYSC Bayan Shekaru 50 Da Kafa Shi?
  • Ya Kamata A Yi Adawa Da Kama Karya A Tabbatar Da Adalci
  • Shugaban Hukumar IAEA Ya Ce JMI Bata Da Makaman Nukliya
  • Ɓarawo ya haɗiye ɗan kunnen Naira biliyan ɗaya
  • Tsohon Gwamnan Oyo, Omololu Olunloyo, Ya Rasu Yana Da Shekaru 89