Kotu ta yanke wa dillalan ƙwayoyi hukuncin ɗaurin shekaru 95
Published: 8th, March 2025 GMT
Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Legas da ta Yola, da Jihar Adamawa, sun yanke wa wasu dillalan miyagun ƙwayoyi huɗu da aka kama da safarar ƙwayoyi da darajarsu ta kai Naira biliyan 4.6 hukuncin ɗaurin shekaru 95 s gidan yari.
Ɗaya daga cikinsu, Ogbuji Christian Ifeanyi, jami’an hukumar NDLEA sun kama shi a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Legas a bara, yana ƙoƙarin shigowa da hodar iblis ɗauri 817 mai nauyin kusan kilogram 20, wadda kuɗinta ya kai biliyan 46.
Sauran da aka kama sun haɗa da Iloduba Augustine Chinonye, Shuaibu Nuhu Isa (wanda aka fi sani da Don), da kuma Zidon Zurga.
Ko da yake, ba wannan ne karo na farko da aka kama Ogbuji ba.
A baya, an kama shi watanni 16 da suka gabata bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi.
Hukuncin Da Kotu Ta YankeBaya ga hukuncin ɗaurin shekaru 95 ko tarar Naira miliyan 25, kotu ta kuma umarci a ƙwace motocin da aka yi amfani da su wajen safarar ƙwayoyin.
A cikin wata sanarwa, mai magana da yawun hukumar NDLEA, Femi Babafemi, ya ce shugaban hukumar, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), ya yaba da hukuncin kotu da kuma ƙoƙarin jami’an NDLEA wajen kama masu safarar miyagun ƙwayoyi a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gidan Yari ƙwayoyi Tara
এছাড়াও পড়ুন:
Gidauniyar Dangote Ta Kai Tallafin Abinci Ga Wadanda Iftila’in Gobara Ya Ritsa Da Su A Jigawa
Mazauna Ƙauyen Batakashi da ke ƙaramar hukumar Garki a Jihar Jigawa sun yaba wa Gidauniyar Aliko Dangote bisa tallafin abinci da ta kai musu.
Wasu daga cikin mazaunan da suka tattauna da wakilinmu sun bayyana farin cikinsu kan wannan karamci, tare da fatan alheri ga gidauniyar.
Daya daga cikin waɗanda suka amfana da tallafin, Malam Umar Abdullahi, ya ce gidauniyar ta kawo sassauci ga al’umma bayan iftila’in gobara da ya cinye gidaje kusan 45 a kwanan nan.
Haka shi ma Malam Usman Auwal, ya nuna farin cikinsa, inda ya yaba da gwamnatin jihar Jigawa da kuma Gidauniyar Dangote, bisa tallafinsu ga al’umma.
A jawabinsa yayin kaddamar da rabon tallafin na buhunan shinkafa guda 500 masu nauyin kilogiram10, Shugaban ƙaramar hukumar Garki, Alhaji Adamu Kore, ya gode wa Gidauniyar Aliko Dangote bisa ƙoƙarinta wajen taimakawa al’umma masu rauni a wannan lokaci da suke cikin bukatar.
Ya bayyana cewa wannan tallafi zai rage wa jama’ar ƙauyen Batakashi raɗaɗin halin da suka shiga sakamakon gobarar.
“Muna matuƙar farin ciki da tallafin Dangote da na gwamnatin jihar Jigawa, domin wannan gudummawa ta faranta ran daruruwan iyalai ba kawai a Jigawa ba har da sauran sassan ƙasar nan gaba ɗaya,” in ji Kore.
A nasa jawabin, Mukaddashin Shugaban Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA), Alhaji Muhammad Murtala, ya ce Gidauniyar Dangote ta kawo buhunan shinkafa 40,000 masu nauyin kilo 10, domin rabawa talakawa da mabukata.
Maiunguwa, wanda kuma shi ne Daraktan Harkokin Gudanarwa da Kuɗi na hukumar, ya ce a ƙarƙashin gwamnatin Namadi, hukumar ta raba tallafi ga al’ummomi da iftila’i ko matsanancin talauci ya shafa.
Wakilin Gidauniyar Aliko Dangote, Alhaji Mustapha Umar, ya ce gidauniyar tana ba da tallafi ga al’ummomi a faɗin Najeriya domin rage wa marasa ƙarfi raɗaɗi.
Ya ce, “Dangote na shirye koyaushe ya taimaka wa ‘yan Najeriya ta hannun Gidauniyar Aliko Dangote, wadda aka ƙirƙira domin aiwatar da ayyukan jinƙai.”
Radio Nigeria ya ruwaito cewa Gidauniyar ta bayar da buhunan shinkafa 500 masu kilo 10 da tabarma 100 ga al’ummar Batakashi da ke yankin Garki a jihar Jigawa, waɗanda gobara ta shafa.
Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa ce ta jagoranci aikin rabon kayan tallafin.
Usman Muhammad Zaria