Aminiya:
2025-03-09@12:02:37 GMT

Kotu ta yanke wa dillalan ƙwayoyi hukuncin ɗaurin shekaru 95 

Published: 8th, March 2025 GMT

Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Legas da ta Yola, da Jihar Adamawa, sun yanke wa wasu dillalan miyagun ƙwayoyi huɗu da aka kama da safarar ƙwayoyi da darajarsu ta kai Naira biliyan 4.6 hukuncin ɗaurin shekaru 95 s gidan yari.

Ɗaya daga cikinsu, Ogbuji Christian Ifeanyi, jami’an hukumar NDLEA sun kama shi a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Legas a bara, yana ƙoƙarin shigowa da hodar iblis ɗauri 817 mai nauyin kusan kilogram 20, wadda kuɗinta ya kai biliyan 46.

Tinubu ya bai wa Farfesa Jega muƙami a gwamnatinsa PDP ta soki dakatar da Natasha, ta nemi a binciki Akpabio

Sauran da aka kama sun haɗa da Iloduba Augustine Chinonye, Shuaibu Nuhu Isa (wanda aka fi sani da Don), da kuma Zidon Zurga.

Ko da yake, ba wannan ne karo na farko da aka kama Ogbuji ba.

A baya, an kama shi watanni 16 da suka gabata bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi.

Hukuncin Da Kotu Ta Yanke

Baya ga hukuncin ɗaurin shekaru 95 ko tarar Naira miliyan 25, kotu ta kuma umarci a ƙwace motocin da aka yi amfani da su wajen safarar ƙwayoyin.

A cikin wata sanarwa, mai magana da yawun hukumar NDLEA, Femi Babafemi, ya ce shugaban hukumar, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), ya yaba da hukuncin kotu da kuma ƙoƙarin jami’an NDLEA wajen kama masu safarar miyagun ƙwayoyi a Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gidan Yari ƙwayoyi Tara

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Ya Yi Kira Da A Kammala Tsare-Tsaren Bunkasa Rundunar Sojin Kasar Sin Na Shekaru 5 Cikin Nasara

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi kira da a aiwatar da matakan da suka wajaba na cimma nasarar tsare-tsare masu inganci, na bunkasa rundunar sojin kasar Sin na shekaru 5, wato tsakanin shekarar 2021 zuwa 2025.

Xi Jinping, wanda kuma shi ne shugaban hukumar zartarwa ta rundunar sojin kasar Sin, kuma sakataren kwamitin kolin JKS, ya yi wannan kira ne a Juma’ar nan, yayin da yake halartar taron rukuni na tawagar rundunar ‘yantar da al’umma ta kasar Sin PLA, da rundunar ‘yan sandan kasar, a wani bangare na taro na uku na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin ta 14. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mun kama ’yan bindiga da suka yi kutse a Kano — ’Yan sanda
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja
  • Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol
  • Hukumar Raya Arewa maso Yamma Ta Kai Ziyara Jihar Jigawa
  • Xi Ya Yi Kira Da A Kammala Tsare-Tsaren Bunkasa Rundunar Sojin Kasar Sin Na Shekaru 5 Cikin Nasara
  • Wani mutum ya yanke jiki ana salla a Masallaci, ya rasu a asibiti
  • Kotu A Kano Ta Yanke Wa Wata Mata Hukunci Kan Safarar Maƙudan Kuɗaɗe
  • Yansanda A Najeriya Sun Kama Yan Kasar Pakistan Biyu Da Hakanni Wajen Sake Yan Kasashen Waje A Kasar
  • Jami’an NDLEA Sun Kashe Budurwa A Kano, An Damƙe Su