HausaTv:
2025-04-08@18:46:27 GMT

Iran : Samar Da Kasashe Biyu Baya Tabbatar Da ‘Yancin Falasdinawa

Published: 8th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araghchi ya sake jaddada kin amincewa da matakin samar da kasashe biyu a matsayin samar da mafita ga rikicin falasdinu, yana mai cewa hakan ba zai tabbatar da hakkokin Falasdinawa ba, a maimakon haka ya ba da shawarar samar da “kasa dimokuradiyya guda daya” a matsayin mafita daya tilo.

Da yake jawabi yayin taron musamman na ministocin harkokin wajen kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC, a birnin Jeddah na kasar Saudiyya da aka kira don magance cin zarafi da laifukan da Isra’ila ke yi kan al’ummar Falasdinu, Araghchi ya jaddada matsayar Iran kan Falastinu tare da bayyana goyon bayan da Tehran ke yi wa Falasdinawa a matsayin abin da ba za a iya mantawa da shi ba.

Araghchi ya kara da cewa, tare da mutunta ra’ayoyin wasu kasashe ‘yan’uwa kan batun samar da kasashe biyu, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta na kan ra’ayinta na cewa, wannan mafita ba za ta kai ga tabbatar da hakkin al’ummar Falastinu ba,” in ji Araghchi, yana mai jaddada matsayin Iran na bayar da shawarar kafa wata kasa ta dimokiradiyya wacce ke wakiltar dukkan ‘yan Falastinu.

Araghchi ya kuma yi kakkausar suka ga yunkurin gwamnatin Amurka na tilasta al’ummar Gaza kaura,” yana mai dagnata hakan da keta dokokin kasa da kasa, da yarjejeniyar Geneva ta hudu.”

Ya kuma bukaci kasashe mambobin kungiyar OIC da su aiwatar da irin wadannan matakai a matsayin wata hanya ta tursasawa gwamnatin sahyoniyawan ta dakatar da laifukan da take aikatawa kan al’ummar Gaza da sauran kasashen yankin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Araghchi ya

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno

Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram ne sun kai hari kauyen Izge da ke Ƙaramar Hukumar Gwoza a Jihar Borno, inda suka kashe sojoji tare da rasa mayaƙansu da dama.

Rahotanni na cewa harin ya auke ne da misalin karfe 1:00 na ranar Lahadi a lokacin da ’yan ta’addan suka mamaye sansanin sojin Nijeriya da ke garin Izge.

Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back An sayar da kare mafi tsada a duniya

Wata majiyar tsaro ta tabbatar wa Aminiya cewar wani soji mai muƙamin Kyaftin da kuma Kofur na daga cikin waɗanda suka kwanta dama, yayin da sojoji suka yi nasarar hallaka mahara da dama a yayin arangamar.

Shugaban ƙaramar Hukumar Gwoza, Hon. Abba Kawu Idrissa Timta, ya tabbatar da faruwar lamarin.

Sai dai ya ce har yanzu lokacin da aka tuntuɓe shi ba a kai ga tantance irin asarar da rayuka daga ɓangarorin biyu ba.

“Sai dai muna tabbatar da kashe ’yan ta’adda da dama,” a cewarsa.

Bayanai sun ce mahara da dama haye a kan babura sun mamaye sansanin sojojin, bayan da suka harba makamin roka da ake kira RPG a kansu.

Rahotanni sun ce, da farko sun kama hanyar nasara a kan sojoji, sai daga bisani mafarauta da ’yan banga suka ƙara ƙwarin guiwa har ta kai ga fatattakar maharan.

Majiyoyi sun ce sojoji da mafarauta da jajirtattun mazauna garin ne suka fatattaki ’yan ta’addan da ke tserewa zuwa dajin Sambisa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran da Amurka zasu fara tattaunawa a Oman ranar Asabar
  • Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa
  • Sabon Tsarin Harajin Kwastam Na Amurka Ya Kwace ‘Yancin Sauran Kasashe
  • Cin Zali Ba Zai Iya Hana Kasashen Afirka Ci Gaba Ba
  • Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno
  • Fedpoly Bauchi Ta Sanya Na’urorin Ɗaukan Hoto ‘CCTV’ Don Daƙile Satar Jarabawa Da Inganta Tsaro
  • Ya Kamata A Yi Adawa Da Kama Karya A Tabbatar Da Adalci
  • Nazarin CGTN: An Bukaci Kasa Da Kasa Su Bijirewa Cin Zali Daga Amurka
  • Sau Biyu Ake Yin Girbin Aya A Shekara – RMRDC
  • Araqchi: Iran ba ta da matsala game da tattaunawa amma ba za ta lamunci yi mata barazana ba