Aminiya:
2025-03-09@12:15:23 GMT

Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar Dattawa

Published: 8th, March 2025 GMT

Majaliar Dattawa ta ce ta dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ne saboda saɓa dokokin majalisar da ta yi, ba don zargin cin zarafin da ta yi wa shugaban majalisar ba.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Sanata Bamidele Opeyemi ne bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar a madadin majalisar.

Kotu ta saki tsohon shugaban Koriya ta Kudu, Yoon Suk Yeol Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano

A cewarsa, dakatar da Sanata Natasha, mataki ne da duka majalisar ta ɗauka, saboda saɓa dokokinta da ta yi kamar yadda kwamitin ɗa’a da ladabtarwa ya tabbatar.

“An dakatar da ita ne saboda yadda take keta dokoki da ƙa’dojin majalisa, da nuna rashin ɗa’a a majalisar, wannan shi ne laifinta babu daɗi babu ragi.”

Sanarwar ta ce da a ce Sanata Natasha ta yi aiki da dokoki da ƙa’idojin majalisar, da majalisar za ta karɓi ƙorafinta, kamar yadda doka ta tanada.

“Amma ba ta bi ƙa’ida da dokokin da suka kafa majalisar da take aiki a cikinta ba.”

Sanata Bamidele ya ce majalisar ta ɗauki matakin dakatar da Sanata Natasha ne bisa shawarar kwamitin ɗa’a, wanda ya same ta da laifin saɓa wa sashe na 6.1 da sashe na 6.2 na dokokin majalisar.

Sanarwar ta kuma zayyano wasu laifuka biyar da ta ce Sanata Natasha ta aikata, ciki har da ƙin zama a kujerar da aka sauya mata a lokacin zaman majalisar na ranar 25 ga watan Fabrairu, da yin magana ba tare da amincewar jagoran zaman majalisar ba, da yin kalaman zagi da rashin girmamawa da shugabancin majalisar.

Aminiya ta ruwaito cewa, a ranar Alhamis da ta gabata ce Majalisar Dattawan Najeriya ta dakatar da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti Uduaghan har na tsawon wattani shida a kan laifin saɓa wa dokokin majalisar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa dakatar da Sanata Natasha majalisar da a majalisar

এছাড়াও পড়ুন:

PDP ta soki dakatar da Natasha, ta nemi a binciki Akpabio

Jam’iyyar adawa ta PDP, ta yi Allah-wadai da dakatar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan bayan ta zargi Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio kan cin zarafinta.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran PDP na Ƙasa, Debo Ologunagba, ya fitar, jam’iyyar ta ce dakatarwar wata hanya ce ta ɓoye zargin da ake yi wa Akpabio.

Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadai Najeriya ta kama hanyar gyaruwa – Remi Tinubu

“Wannan mataki ba wai kawai ya hana Sanata Akpoti-Uduaghan damar kare kanta ba ne, har ma yana nuna cewa majalisar na kare rashin ɗa’a,” in ji PDP.

Jam’iyyar ta kuma ce dakatarwar ba adalci ba ce ga al’ummar yankin Kogi ta Tsakiya, waɗanda yanzu suka rasa wakilci a majalisa.

“Wannan cin zarafi ne da amfani da muƙami ba daidai ba, domin Akpabio na ci gaba da zama a kujerarsa duk da irin wannan zargi mai girma.

“Idan har bai da abin ɓoyewa, ya sauka don bayar da damar gudanar da bincike na gaskiya,” in ji PDP.

PDP ta nuna cewa ba wannan ne karon farko da ake zargin Akpabio da aikata irin wannan ba.

Ta ce tsohuwar Shugabar Hukumar Raya Yankin Neja Delta (NDDC), Dokta Joi Nunieh, ta taɓa yin irin wannan ƙorafi a kansa.

Jam’iyyar ta buƙaci Shugaban Majalisar Dattawa da ya kare sunansa ta hanyar amincewa da bincike maimakon ƙoƙarin ɓoye gaskiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • BUK Ta Kori Ɗalibai 62, Ta Dakatar da 17 Saboda Satar Jarrabawa
  • Rikicin Shugabancin Majalisar Legas: Ko Sulhunsu Zai Dore?
  • PDP ta soki dakatar da Natasha, ta nemi a binciki Akpabio
  • Zan sasanta Akpabio da Natasha — Ministar Harkokin Mata
  • Dakatarwa: Har yanzu ni Sanata ce — Natasha
  • Majalisar Dattawa Ta Dakatar Da Sanata Natasha Na tsawon Watanni 6 Saboda Rashin Da’a
  • Majalisar Dattawa ta dakatar da Sanata Natasha na Watanni 6
  • Ƴar Majalisar Dattawa Natasha Akpoti Na Fuskantar Dakatarwar Wata Shida
  • Majalisar Dattawa na shirin dakatar da Natasha na wata 6