Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu
Published: 9th, March 2025 GMT
Iyalan marigayi Janar Sani Abacha, sun gargaɗi Tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Babangida, da ya daina faɗin maganganun da ka iya ɓata sunan mahaifinsu.
A cikin wata sanarwa da Mohammed Abacha, ya fitar a madadin iyalan marigayin a ranar Lahadi, sun musanta iƙirarin da Babangida ya yi a cikin littafinsa mai suna ‘A Journey in Service’.
Ya ce Janar Abacha ne, ya ke da alhakin soke zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga wata Yunin 1993.
“Duk wani yunƙuri na ɗora wa Janar Sani Abacha laifin soke zaɓen, wanda a lokacin ya kasance babban jami’in soja a mulkin Babangida, ƙoƙari ne na sauya tarihi da gangan.
“Shekaru da dama, wasu mutane na ƙoƙarin ɓata haƙiƙanin abin da ya faru a wannan lokaci a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya,” in ji sanarwar.
Iyalan Abacha sun jaddada cewa a lokacin da aka soke zaɓen, Janar Abacha ba shi ne Shugaban Ƙasa ko Babban Kwamandan Askarawan Najeriya ba.
Sun ce Babangida ne, ya ke da cikakken iko, kuma shi kaɗai ne ke da alhakin duk wani hukunci da gwamnatinsa ta yanke.
“Hukuncin soke zaɓen ya fito ne daga gwamnatin Janar Ibrahim Babangida, wanda yake a matsayin Shugaban Ƙasa, yana da cikakken iko kuma shi ne ke da alhakin duk wani abu da gwamnatinsa ta aikata,” in ji sanarwar.
Haka kuma, iyalin Abacha sun yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji “ƙagaggun labarai da ake ƙirƙira don karkatar da tunanin jama’a saboda wasu muradu na siyasa ko na ƙashin kai.”
Sun jaddada cewa, “Ba za mu yarda a ɓata tarihin mahaifinmu da wasu zarge-zargen banza da aka ƙirƙira don kare waɗanda suka aikata laifin ba.”
“Mun kuma ga dacewar tunatar da mutane cewa a lokacin da rayuwar Janar Babangida ta shiga hatsari, Janar Abacha ne, ya kawo masa ɗauki, ya tabbatar da cewa ba a cutar da shi ba,” in ji iyalan.
A ƙarshe, sun soki littafin ‘A Journey in Service’, inda suka ce littafin bai bayar da sahihin tarihin abubuwan da suka faru ba.
“A cewar wani da ya yi sharhi a kan littafin, gaskiya, amana ba halaye ba ne da za a alaƙanta su da marubucin ba,” in ji su.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gargadi iyalai soke zaɓen
এছাড়াও পড়ুন:
Makahon da ke sana’ar POS
Isyaku Mahmud, makaho ne dan shekara 28 da ke sana’ar sayar da data a yankin Kudancin Kaduna.
Ya shaida wa Aminiya cewa har sana’ar hada-hadar kudi ta POS yana yi a baya, amma yanzu ba shi da jari.
Ta’addancin yankin Sahel ya ninka na sauran sassan duniya — Rahoto Yadda masana’antun Arewa suka koma kufaiAminiya ta ga yadda makahon yake sarrafa manhajojin WhatsApp is Fesbuk kuma yake sayar da data kai tsaye daga wayarsa ta hanyar amfani da tsarin Smart Cash tare da tura kudi da wayar tasa, kamar yadda ya gwadawa wakilinmu.
Dan asalin garin Yalwa da ke Karamar Hukumar Tudun Wada (Dan Kadai) da ke Jihar Kano ne, ya kwashe shekaru kusan biyar yana zuwa yawon bara a garin Kafanchan da ke Jihar Kaduna.
Aminiya ta samu zantawa da shi, inda ya gwada duk abubuwan da yake yi da wayarsa ciki, har da lalubo wakar da ya yi ya kuma tura cikin wani zaure na mawaƙa ba tare da wani ya nuna masa ko ya taimaka ba.
Yana iya kuma tattaunawa da kowa ta hanyar sauti a manhajar WhatsApp tunda bai iya rubutu ba.
Amma da kansa yake budewa ya lalubo wanda yake son tura wa da sako kuma ya tura masa.
“Ka san ina yin wakokin yabon Manzon Allah. Idan na samu ƙarin baitin sai na ɗauko wayata na rera tunda ba zan iya rubutawa ba.
“Idan na gama hada adadin baitukan da nake so akwai dalibai ’yan Islamiyya, sai na ba su muje inda ake buga wakoki a studiyo, sai su hau su rera.
“Ba ni nake rerawa ba, amma duka wakokina ne. A can garinmu nake wannan kuma a yanzu haka ina da kasidu da aka buga sun haura guda 20.
“An haife ni ne a shekarar 1997, an shaida min cewa an haife ni da idanu na garai, amma bayan an yaye ni, a shekarar sai mahaifiyata ta rasu kuma tun daga nan sai na daina gani, wato na makance, shine har zuwa yau kuma,” in ji shi.
Ya ce ya yi karatun tsangaya kafin daga baya aka matsa masa cewa sai ya fita yawon bara.
“Saboda haka ba a son raina nake bara ba, amma a lokacin babu wani abu da zan iya yi. Wannan ya faru ne a shekarar 2012 tun lokacin nake bara.”
Ya ce da zai samu wani tallafi na jari, a shirye yake ya yi wasu sana’o’i ko buɗe shagon harkar POS ko wani abu da zai iya dogaro da shi musamman yanzu da yake da yara ƙananan guda biyu da yake son su samu kulawa ta musamman tare da yin karatu mai zurfi.
“Ina da mata daya da ƙananan yara guda biyu kuma gaskiya ina son su yi karatu duka na addini da na boko.”