Aminiya:
2025-04-09@05:45:52 GMT

Iyalan Abacha sun gargaɗi Babangida kan ɓata sunan mahaifinsu

Published: 9th, March 2025 GMT

Iyalan marigayi Janar Sani Abacha, sun gargaɗi Tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Babangida, da ya daina faɗin maganganun da ka iya ɓata sunan mahaifinsu.

A cikin wata sanarwa da Mohammed Abacha, ya fitar a madadin iyalan marigayin a ranar Lahadi, sun musanta iƙirarin da Babangida ya yi a cikin littafinsa mai suna ‘A Journey in Service’.

Ramadan: Ali JC ya bai wa jama’a tallafin kayan abinci a Gombe An samu tsohon shugaban hukumar tsaron Faransa da zamba

Ya ce Janar Abacha ne, ya ke da alhakin soke zaɓen shugaban ƙasa na ranar 12 ga wata Yunin 1993.

“Duk wani yunƙuri na ɗora wa Janar Sani Abacha laifin soke zaɓen, wanda a lokacin ya kasance babban jami’in soja a mulkin Babangida, ƙoƙari ne na sauya tarihi da gangan.

“Shekaru da dama, wasu mutane na ƙoƙarin ɓata haƙiƙanin abin da ya faru a wannan lokaci a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya,” in ji sanarwar.

Iyalan Abacha sun jaddada cewa a lokacin da aka soke zaɓen, Janar Abacha ba shi ne Shugaban Ƙasa ko Babban Kwamandan Askarawan Najeriya ba.

Sun ce Babangida ne, ya ke da cikakken iko, kuma shi kaɗai ne ke da alhakin duk wani hukunci da gwamnatinsa ta yanke.

“Hukuncin soke zaɓen ya fito ne daga gwamnatin Janar Ibrahim Babangida, wanda yake a matsayin Shugaban Ƙasa, yana da cikakken iko kuma shi ne ke da alhakin duk wani abu da gwamnatinsa ta aikata,” in ji sanarwar.

Haka kuma, iyalin Abacha sun yi kira ga ‘yan Najeriya da su guji “ƙagaggun labarai da ake ƙirƙira don karkatar da tunanin jama’a saboda wasu muradu na siyasa ko na ƙashin kai.”

Sun jaddada cewa, “Ba za mu yarda a ɓata tarihin mahaifinmu da wasu zarge-zargen banza da aka ƙirƙira don kare waɗanda suka aikata laifin ba.”

“Mun kuma ga dacewar tunatar da mutane cewa a lokacin da rayuwar Janar Babangida ta shiga hatsari, Janar Abacha ne, ya kawo masa ɗauki, ya tabbatar da cewa ba a cutar da shi ba,” in ji iyalan.

A ƙarshe, sun soki littafin ‘A Journey in Service’, inda suka ce littafin bai bayar da sahihin tarihin abubuwan da suka faru ba.

“A cewar wani da ya yi sharhi a kan littafin, gaskiya, amana ba halaye ba ne da za a alaƙanta su da marubucin ba,” in ji su.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gargadi iyalai soke zaɓen

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato

Gwamnatin Sakkwato ta yi barazanar sanya ƙafar wando da waɗanda ta yi zargi suna ƙoƙarin kawo mata cikas a yaƙin da take yi da ’yan bindiga da sauran matsalolin tsaro a Jihar.

Ta gargaɗi mazauna da su shiga taitayinsu game da yin kalamai da za su iya kawo cikas ga ƙoƙarinta na magance matsalar rashin tsaro a jihar.

Wannan gargaɗin ya biyo bayan wata sanarwa da ake dangantawa wani mai suna Basharu Altine Guyawa wanda ya yi ƙoƙarin nuna cewa gwamnati ba ta yi abin da ya kamata ba a fannin tsaro.

Mai ba Gwamna Ahmed Aliyu shawara na musamman kan harkokin tsaro, Kanar Ahmed Usman mai ritaya, ya yi wannan gargaɗin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Mahara sun yi garkuwa da fiye da mutum 50 a Katsina NAJERIYA A YAU: Dabarun Samun Kuɗaɗe Ta Hanyar Amfani Da Wayar Hannu

Usman ya ce irin wannan kalaman suna iya sanya mutane butulce wa abin da gwamnati da jami’an tsaro suke yi wajen kawo ƙarshen matsalar tsaro a jihar.

Ya ce “Ya kamata mutanenmu su guji yin magana da tayar da hankali da kuma siyasantar da matsalar tsaro. A maimakon haka, ya kamata su goyi bayan gwamnati a ƙoƙarinta na neman hanyoyin magance matsalolin tsaronmu na dindindin.

“Gwamnati ba za ta lamunci duk wani yunƙurin wani mutum ko ƙungiya na kawo cikas ga ƙoƙarinta ko kuma shagaltar da ita a wannan batun ba.

“Gwamnatin jihar tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro sun kasance suna aiki tuƙuru don maido da zaman lafiya, musamman a yankin gabashin jihar da ke fuskantar ƙalubalen tsaro.

“Gwamnati kwanan nan ta yi wani aiki na haɗin gwiwa a yankin wanda ya samu gagarumar nasara yayin da aka lalata maboyar ’yan bindiga da dama da aka gano tare da kashe ’yan ta’adda da dama a cikin aikin. Bugu da ƙari, an kuma ceto daruruwan waɗanda aka yi garkuwa da su a lokacin aikin.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijar ta ayyana Hausa a matsayin yaren ƙasa
  • DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa ‘Matar Bahaushe Ba Ta Iya Kiran Sunan Mijinta’
  • Kisan Janar Alƙali: Kotu ta ɗage shari’a zuwa 28 ga Mayu
  • Matsalar tsaro: Ba za mu lamunci zagon ƙasa ba — Gwamnatin Sakkwato
  • Kasar Sin Ta Nanata Kudurinta Na Ci Gaba Da Bude Kofa Yayin Wani Taro Da Kamfanonin Amurka 
  • Jam’iyyar Labour Ta Yi Barazanar Dakatar Da Peter Obi Da Gwamna Otti
  • An sayar da kare mafi tsada a duniya
  • ’Yan sanda sun janye gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah
  • ’Yan sanda sun soke gayyatar da suka yi wa Sanusi II kan hawan sallah
  • Ba Rabo Da Gwani Ba: Abdullahi Karkuzu 1931-2025