Leadership News Hausa:
2025-04-09@06:02:39 GMT

Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Za Ta Ba Mata Damar Cimma Burikansu

Published: 9th, March 2025 GMT

Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Za Ta Ba Mata Damar Cimma Burikansu

Ofishin jakadancin kasar Sin dake Nijeriya, ya shirya taro domin bikin ranar mata ta duniya da ake gudanarwa a ranar 8 na watan Maris din kowacce shekara. Taron mai taken “Labarinta, Makomarta” wanda ya gudana ranar Juma’a a cibiyar raya al’adu ta kasar Sin dake birnin Abujan Nijeriya, ya hada mata daga dukkan bangarorin rayuwa, inda suka yi waiwaye kan ci gaban da suka samu da ma tsara hanyar tabbatar da daidaiton jinsi.

  

Da yake jawabi yayin taron, jakadan Sin a Nijeriya Yu Dunhai, ya nanata muhimmancin bikin na wannan shekara kasancewar ya zo daidai da cikar Yarjejeniyar Beijing ta tabbatar da daidaiton jinsi ta MDD, shekaru 30 da kulluwa.

A Mai Da Duniya Ta Zama Ta Kasa Da Kasa Shugabannin Larabawa Sun Amince Da Tsarin Gina Gaza Da Zai Lakume Dala Biliyan 53

Ya kara da cewa, “Sin za ta hada hannu da Nijeriya wajen kyautata aiwatar da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da aiwatar da shirye-shiryen hadin gwiwa 10 dake tsakaninsu, ciki har da inganta musaya tsakanin mata da hada hannu wajen gina al’ummar Sin da Nijeriya mai makoma ta bai daya. Ya kara da cewa, ya yi imani mata da dama za su amfana tare da cimma burikansu da samar da kyakkyawar makoma ta hanyar ingantaccen hadin gwiwar Sin da Nijeriya, karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya.

A nasa jawabi, mukaddashin babban sakataren ma’aikatar raya al’adu da fasahohi da bude ido da tattalin arzikin bangaren, Oraeluno Rapheal, ya kara tabbatar da goyon bayan da gwamnatin kasar ke bayarwa ga ci gaban harkokin mata. Ya ce Nijeriya za ta ci gaba da tabbatar da inganta kwarewar mata ta hanyar bayar da horo da musayar al’adu da sauran shirye-shiryen dake da zummar ba mata damar kara taka rawar gani. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: da Nijeriya tabbatar da Da Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Manufar Hade Aikin Raya Larduna Ita Ce Mabudin Kofar Cimma Zamanantarwa Da Samun Wadata 

Muhimmin jigon dabarar raya yankunan a tare shi ne, bude kofar cimma zamanantarwa da samun wadata na bai daya ga dukkan jama’a. (Fa’iza)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Na Yaki Da Cin Zalin Da Amurka Ke Yi Ta Hanyar Dora Haraji Ne Bisa Sanin Ya Kamata
  • Kasar Sin Za Ta Inganta Aminci Da Hadin Gwiwa A Asiya
  • Li Qiang Ya Tattauna Da Shugabar Kwamitin EU
  • HKI Ta Kara Yawan Hare-Hare A Kan Gaza A Dai Dai Lokacinda Ake Kiranta Zuwa Tsagaita Wuta
  • Sin Za Ta Mai Da Martani Kan Barazanar Kara Kakkaba Mata Harajin Kwastam Daga Amurka  
  • Najeriya: An gudanar da zanga-zangar adawa da wasu shirye-shiryen  gwamnati
  • Manufar Hade Aikin Raya Larduna Ita Ce Mabudin Kofar Cimma Zamanantarwa Da Samun Wadata 
  • Sin Ta Gabatar Da Dabarunta Na Raya Sana’o’i Da Fasahohi Masu Kiyaye Muhalli Ga Taron WTO
  • Araqchi: Iran ba ta da matsala game da tattaunawa amma ba za ta lamunci yi mata barazana ba
  • An yi wa wata mata ƙarin jini sau 36