Mayar da hankali kan taruka biyu na kasar Sin, wato taron majalisar wakilan jama’ar kasar (NPC) da kuma taron majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar (CPPCC), muhimmin abu ne ga manyan shugabannin kamfanonin kasashen waje dake kasar Sin.

Zuwa karshen shekara ta 2024, adadin kamfanonin da baki ’yan kasashen waje suka zuba jari don kafa su a kasar Sin, ya zarce miliyan 1.

239. A matsayinsu na wadanda ke gane wa idanunsu, da wadanda ke bayar da gudummawa, gami da wadanda ke cin moriya, daga harkokin yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje na kasar Sin, kamfanonin jarin waje sun riga sun bada hadin-kai tare da samun ci gaba tare da bunkasar tattalin arzikin kasar Sin.

A wajen tarukan biyu da aka gudanar a wannan watan da muke ciki, an bullo da wasu ingantattun manufofi, wadanda suka karfafa gwiwar kamfanonin jarin waje. A cikin rahoton aikin gwamnati na bana, an mayar da “fadada bude kofa ga kasashen waje, da tabbatar da ci gaban cinikin waje da jarin waje yadda ya kamata” a matsayin daya daga cikin muhimman ayyuka 10 na gwamnatin kasar Sin a shekara ta 2025. Tun daga fadada bangarorin da suka shafi sadarwa, likitanci da ilimi, har zuwa karfafa gwiwar masu zuba jari na kasashen waje don su kara zuba jari, da tabbatar da hakkokin kamfanonin waje dake kasar Sin, da kuma inganta yanayin gudanar da kasuwanci a kasar, akwai alamu da dama dake shaida cewa, kasar Sin na habaka bude kofarta ga kasashen ketare, kana, jarin waje na kara fuskantar damarmaki a kasar ta Sin.

Ana ci gaba da bullo da wasu nagartattun manufofi a kasar Sin, al’amarin dake janyo karin damarmaki. Don haka, yanzu lokaci ne mafi dacewa ga kamfanonin jarin waje su gudanar da ayyuka a kasar Sin, inda bangarorin biyu za su ci moriya tare. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasashen waje a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar da cewa, bisa gayyatarsa da sakatare janar na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Vietnam kuma shugaban jamhuriyar gurguzu ta Vietnam ya yi, shugaban kasar Sin Xi Jinping, zai kai ziyarar aiki kasar daga ranar 14 zuwa 15 ga wata.

 

Haka kuma, bisa gayyatarsa da firaministan kasar Malaysia da sarkin Cambodia suka yi, shugaban na kasar Sin kuma sakatare janar na JKS, zai ziyarci kasashen Malaysia da Cambodia daga ranar 15 zuwa 18 ga wata. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Xi Jinping Zai Ziyarci Kasashen Vietnam Da Malaysia Da Cambodia
  • Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m
  • An Kafa Dokar Kai Da Komowa A Kudancin Kasar Syria
  • Iran Da Armenia Suna Fara Atisayen Hadin Giwa Don Karfafa Tsaron   Kan Iyakar Kasashen Biyu
  • Kasashen China Da EU Sun Maida Martani Kudin Fito Kan Kasar Amurka
  • Huawei Ya Daddale Yarjejeniya Da Kenya Don Habaka Kwarewar Ma’aikatan Kasar A Fannin Dijital
  • Sin Ta Kara Wasu Kamfanonin Amurka 12 Cikin Jerin Wadanda Ta Dakatar Da Fitar Musu Da Wasu Kayayyaki Daga Kasar Sin
  • Yadda Kasashen Afirka Za Su Iya Rage Illar Harajin Amurka
  • Zuba Jari Daga Kasashen Waje A Noman Zamani: Jigawa Ta Baje Kolin Aikin Noma A Abuja