Mayar da hankali kan taruka biyu na kasar Sin, wato taron majalisar wakilan jama’ar kasar (NPC) da kuma taron majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar (CPPCC), muhimmin abu ne ga manyan shugabannin kamfanonin kasashen waje dake kasar Sin.

Zuwa karshen shekara ta 2024, adadin kamfanonin da baki ’yan kasashen waje suka zuba jari don kafa su a kasar Sin, ya zarce miliyan 1.

239. A matsayinsu na wadanda ke gane wa idanunsu, da wadanda ke bayar da gudummawa, gami da wadanda ke cin moriya, daga harkokin yin gyare-gyare a gida da bude kofa ga kasashen waje na kasar Sin, kamfanonin jarin waje sun riga sun bada hadin-kai tare da samun ci gaba tare da bunkasar tattalin arzikin kasar Sin.

A wajen tarukan biyu da aka gudanar a wannan watan da muke ciki, an bullo da wasu ingantattun manufofi, wadanda suka karfafa gwiwar kamfanonin jarin waje. A cikin rahoton aikin gwamnati na bana, an mayar da “fadada bude kofa ga kasashen waje, da tabbatar da ci gaban cinikin waje da jarin waje yadda ya kamata” a matsayin daya daga cikin muhimman ayyuka 10 na gwamnatin kasar Sin a shekara ta 2025. Tun daga fadada bangarorin da suka shafi sadarwa, likitanci da ilimi, har zuwa karfafa gwiwar masu zuba jari na kasashen waje don su kara zuba jari, da tabbatar da hakkokin kamfanonin waje dake kasar Sin, da kuma inganta yanayin gudanar da kasuwanci a kasar, akwai alamu da dama dake shaida cewa, kasar Sin na habaka bude kofarta ga kasashen ketare, kana, jarin waje na kara fuskantar damarmaki a kasar ta Sin.

Ana ci gaba da bullo da wasu nagartattun manufofi a kasar Sin, al’amarin dake janyo karin damarmaki. Don haka, yanzu lokaci ne mafi dacewa ga kamfanonin jarin waje su gudanar da ayyuka a kasar Sin, inda bangarorin biyu za su ci moriya tare. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kasashen waje a kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Ghana ya ziyarci kasashen Sahel da suka balle daga Ecowas

Shugabana kasar Ghana John Dramani Mahama, ya ziyarci kasashen Mali da Nijar a wani bangare na ran gadin diflomatsiyya da ya fara a kasashen sahel din nan uku da suka balle daga kungiyar Ecowas.

Bayan birnin Bamako a ranar Asabar, shugaban kasar Ghana John Dramani Mahama ya je birnin Yamai a ranar Lahadi, inda wasu rahotanni ke cewa ya je ne da nufin dinke barakar da ke tsakanin kungiyar ta raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) da kasashen uku na Sahel.

Saidai a cikin wata sanarwa da aka karanta a gidan talabijin na Nijar, hukumomin kasar sun tabbatar da cewa kasashen sun tabbatar da aniyarsu ta karfafa dangantakar abokantaka da hadin gwiwa a tsakanin kasashensu a fannonin siyasa, tattalin arziki da tsaro.

Kafin Nijar, John Dramani Mahama ya je Mali inda Janar Assimi Goïta ya tarbe shi. A cewar fadar shugaban kasar Ghana, ganawar da aka yi tsakanin mutanen biyu ta ba da damar fara tattaunawa kan karfafa hadin gwiwa a fannin tsaro.

Shugaban na Ghana ya kuma yi amfani da wannan dama wajen bayyana mahimmancin kasuwanci ta hanyar hanyar tashoshin jiragen ruwa na Ghana da ke Tekun Atlantika ga Mali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Ruwa Na Kasashen Rasha Da China Sun Shigo Kasar Iran Don Fara Atisayen Sojojin Ruwa Mai Suna “Damarar Tsaro 2025”
  • Rasha Ta Ce Babu Wani Abinda Zai Maye Gurbin  Yarjejeniyar JCPOA Ta Shirin Nukliyar Kasar Iran
  • Shugaban Ghana ya ziyarci kasashen Sahel da suka balle daga Ecowas
  • Isra’ila ta katse wutar lantarki a zirin Gaza
  • Hadin Gwiwar Sin Da Nijeriya Za Ta Ba Mata Damar Cimma Burikansu
  • Sharhin Bayan Labarai: Kasashen Afirka Sun Kori Sojojin Faransa Daga Kasashensu
  • Qatar Ta Ce Bata Goyon Bayan Yakin Don Warware Shirin Nukliyar Kasar Iran
  • Aragchi: Hare-hare Kan Cibiyoyin Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Ba Za Su Wargaza Shirin Ba
  • Fararen hula 162 sun rasa rayukansu a tashe-tashen hankulan a lardunan gabar tekun Syria