Araghchi: Gwamnatin Amurka ta haramta wa Irakawa samun wutar lantarki
Published: 11th, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi Allah-wadai da matakin da gwamnatin Amurka ta dauka na haramtawa al’ummar Iraki ‘yancinsu na samun wutar lantarki, da ma wasu ababen more rayuwa.
“Muna tare da al’ummar Iraki, kuma mun tabbatar da alkawarinmu ga gwamnatin Iraki na ba da hadin kai wajen tinkarar matakan da Amurka ta dauka ba bisa ka’ida ba,” in ji Araghchi a wani sakon da ya wallafa a shafin X.
Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto wani babban jami’an makamashi a kasar Iraki yana cewa, a halin yanzu Iraki ba ta da wasu hanyoyin da za su maye gurbin makamashin da ake shigowa dashi daga kasar Iran, lamarin da zai haifar da babban kalubale wajen biyan bukatar wutar lantarki a cikin gida musamman a lokacin bazara.
Tun da farko a ranar Lahadin da ta gabata, wani jami’in Amurka ya tabbatar da cewa Washington ta yanke shawarar kin sabunta yarjejeniyar da ta bai wa Iraki damar sayen wutar lantarki daga Iran.
Wani babban jami’in ma’aikatar wutar lantarki ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa “Gwamnati ta fara aiwatar da matakan gaggawa don rage tasirin matakin da Amurka ta dauka kan samar da wutar lantarki a Iraki.”
Wa’adin ya kare a ranar Asabar din da ta gabata, yayin da kumama’aikatar harkokin wajen Amurka ba ta tsawaita wa’adin ba, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin jakadancin Amurka da ke Bagadaza ta bayyana.
Wannan shawarar wani bangare ne na matakin matsin lamba na Shugaba Donald Trump kan Iran, da nufin dakatar da abin da yake kira barazanar nukiliyar Iran, da dakile shirinta na makami mai linzami da kuma hana ta tallafawa kungiyoyin ‘yan gwagwarmaya a yankin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha Ta Ce Babu Wani Abinda Zai Maye Gurbin Yarjejeniyar JCPOA Ta Shirin Nukliyar Kasar Iran
Jakadan kasar Rasha na din din din a cibiyoyin MDD da suke Vienna, ya bayyana cewa dakatar da aiwatar da yarjeniyar shirin Nukliya na kasar Iran wanda ake kira JCPOA, wacce kuma aka samar da shi a shekara ta 2015, da kasashen yamma suka yi, shi ne ya haddasa dukkan matsalolin da suka biyo baya.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto, Mikhail Awliyonov yana fadar haka a hirar da ta hada shi da jaridar Ezustiyo na kasar Rasha.
Jakadan ya kara da cewa a tsakanin shekara ta 2021 da kuma 2022 an tattauna da kasashen yamma kan yadda za’a aiwatar da yarjeniyar JCPOA da kasashen bayan da kasar Amurka ta fice daga yarjeniyar a shekara ta 2018, amma sai kasashen yamma suka yi watsi da ita sannan suka dorawa kasar Iran sabbin takunkuman tattalin arziki. Jakadan ya kuma kara da cewa a halin yanzu ba za’a warware wadannan matsalolin da suke tasowa kan shirin Nukliyar kasar Iran ba, sai an dawo kan yarjejeniyar ta JCPOA, sannan wadannan kasashen su mayarwa Iran hakkokinta da suka take a cikinta, wadanda suka kaita ga maida martanin da ta yi.
Ya ce, a halin yanzu shekaru ukku sun gabata da yin watsi da yarjeniyar, sannan har yanzun kasar Iran bada sabawa yarjeniyar ba, wanda ya kai ga yarjeniyar zata mutu a cikin watan Octoban shekara ta 2025 da muke ciki. Jakadan ya ce har yanzun ba’a da wani abu da zai maye gurbin yarjeniyar ta JCPOA. Wanda ke samun goyon bayan kudurin kwamitin tsaro na MDD mai lamba 2231.