Lakurawa sun kashe mutum 13 a ƙauyukan Kebbi
Published: 11th, March 2025 GMT
Mayaƙan Lakurawa sun kashe mutum 13 a wani harin ramuwar gayya da suka kai yankin Birnin Debe da ke Ƙaramar Hukumar Arewa a Jihar Kebbi.
Wani mazauni mai suna Musa Gado, ya ce maharan wanda suka kai harin a ranar Lahadi, sun kuma ƙone ƙauyuka takwas daga cikin tara da ke yankin.
Tsohon shugaban Philippines ya faɗa komar ’yan sanda Jihohi 12 da za a fuskanci tsananin zafin rana — NiMetShi ma wani mazaunin yankin, Suleiman Abubakar wanda ya rasa ɗan uwansa ɗaya a dalilin harin, ya ce maharan sun auka wa ƙauyukan ne da yammaci bayan sallar Magariba.
“Abin ba a cewa komai domin mun ga tashin hankali. Sun kashe mutane da dama sun ƙone mana ƙauyuka kuma babu wanda suka ƙyale hatta mata da ƙananan yara.”
Aminiya ta ruwaito cewa, galibin waɗanda suka jikkata a dalilin harin yanzu haka suna samun kulawa a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Birnin Kebbi.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Arewa, Sani Aliyu, ya tabbatar da faruwar lamari da cewa tuni an tura ƙarin jami’an tsaro zuwa yankin yayin da gwamnatin ke ci gaba da ɗaukar mataki a kan lamarin.
Harin wanda ake zargin na ramuwar gayya ne na zuwa ne bayan wani farmakin haɗin gwiwa tsakanin jami’an tsaro da gwamnatin Kebbi, wanda ya yi sanadin mutuwar wani shugaban ’yan ta’addar Lakurawa da ake kira Maigemu.
Majiyoyin leƙen asiri sun tabbatar da cewa an kashe Maigemu a yankin Kuncin Baba da ke Arewacin jihar, bayan fafatawar da aka yi a ranar Alhamis ta makon jiya.
Da take martani, rundunar ’yan sandan jihar, ta ce mayaƙan Lakurawa ne suka kai harin a yankunan Birnin Debi, Dogon Daji, Danmarke, Yar Goru, Tambo, Garin Nagoro da kuma Garin Rugga da ke Arewacin jihar.
Rundunar ta ce mayaƙan ɗauke da muggan makamai sun kai hari a waɗannan yankunan da ke iyaka da Jamhuriyyar Nijar, inda suka kashe aƙalla mutum 11 yayin da wasu biyu suka jikkata.
Wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar ta ce maharan sun koma ƙone wasu gida ƙurmus a ƙauyukan da abin ya shafa.
Ana iya tuna cewa, a watan jiya na Fabarairu ne wasu ’yan ta’addan suka kashe wani mutum tare da jikkatar wasu shida a yayin harin da aka kai ƙauyen Gulman da ke Ƙaramar Hukumar Argungu ta Jihar Kebbi.
Kazalika, mayaƙan ake ɗora wa alhakin kashe wasu jami’an hukumar shige da fice biyu da wani farar hula ɗaya a Ƙaramar Hukumar Kangiwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Kebbi Lakurawa Ƙaramar Hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun ceto mafiya 16 da aka yi garkuwa da wasu a Filato
Sojoji a Jihar Filato sun ceto wasu mutum 16 da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su a kan titin Jos zuwa Mangu.
Dakarun Rundunar Operation Safe Haven ne suka ceto mutanen a cikin wata mota da a aka jefar da ita a yankin Mararabar Kantoma da ke Ƙaramar Hukumar Manngu.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Manjo Samson Zakhom, ya bayyana cewa an ceto mutanen ne da misalin ƙarfe 9 na dare bayan sun tsinci motar a daji babu kowa a ciki.
Ya ce ganin haka ne sojojin rundunar da ke aikin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a jihar suka yi zargin sace fasinjojin cikinta aka yi.
An yi garkuwa da masu ibada a Kogi Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar FilatoManjo Samson Zakhom ya ce sojojin suna tsaka da bincike sai ’yan bindigar suka buɗe musu wuta, inda bayan arangamar ɓata-garin suka tsere suka bar matafiyan.
Ya bayyana cewa, a cikin fasinjojin 16 da aka ceto har da ƙananan yara guda shida, kuma duk a ba sau taimakon farko saboda raunukan da suka samu, sannan muka raka su, suka ci gaba tafiyarsu.”