Aminiya:
2025-04-12@07:30:06 GMT

Ba abin da zai faru idan aka tsige Fubara – Wike

Published: 12th, March 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Ribas kuma Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya ce idan buƙatar tsige Gwamna Siminalayi Fubara ta zama tilas za a iya yi.

Wike ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai a ranar Laraba, inda ya jaddada cewa siyasa ba wasa ba ce, kuma ya kamata a bi ƙa’ida wajen tafiyar da mulki.

Zulum ya bai wa ƙananan ’yan kasuwa tallafin 1bn a Borno HOTUNA: An hana Gwamna Fubara shiga Majalisar Dokokin Ribas

Hakazalika, ya soki maganar cewa ‘yan majalisa ƙalilan za su iya zama domin yin dokokin jiha.

“Siyasa ba wasa ba ce. Idan har ya aikata abin da ya cancanci a tsige shi, to sai a tsige shi. Ba laifi ba ne,” in ji Wike.

“Ba zan yarda cewa a cikin wannan ƙasa, mutane na tunanin ‘yan majalisa uku za su zauna su yi doka, sannan su ce suna shirin zuwa Kotun Ƙoli.

“Shin har yanzu muna buƙatar yin aiki?” ya tambaya.

Rigimar siyasa a Jihar Ribas ta tsananta bayan da Kotun Ƙoli ta amince da sahihancin ‘yan majalisa 27 da ke goyon bayan Wike tare da soke zaɓen ƙananan hukumomin da aka gudanar a watan Oktoban 2024.

Har ila yau, Wike ya jinjina wa waɗanda suka ƙalubalanci abin da ya kira rashin bin doka, inda ya bayyana cewa dole ne a mutunta zaɓaɓɓun shugabanni.

“Shugabannin majalisa da ‘yan majalisa ba yara ba ne; an zaɓe su ne, kuma ba yaran kowa ba ne.

“Ya kamata a zauna da su, a gina dangantaka da su,” in ji shi.

Alaƙa dai na ci gaba da zafi tsakanin Wike da yaronsa Fubara, tun bayan da bar mulkin Jihar Ribas.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Fubara Siminalayi Fubara Siyasa yan majalisa

এছাড়াও পড়ুন:

Sin: Idan Har Amurka Na Son Tattaunawa, Ya Zama Wajibi Ta Dakatar Da Aiwatar Da Matakan Gangaci

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahaifi ya yi wa ’yarsa ciki a Bauchi
  • Sin: Idan Har Amurka Na Son Tattaunawa, Ya Zama Wajibi Ta Dakatar Da Aiwatar Da Matakan Gangaci
  • UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi
  • Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi
  • ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
  • Ruwan sama ya lalata gidaje da yawa a Kebbi
  • Babu Wani Saɓani Tsakanin Tinubu Da Shettima — Jigon APC
  • Gwamnan Zamfara Ya Yi Jajen Rasuwar Dan Majalisa Aminu K/Daji
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Iran Ba Zata Jada Bayan Ba A Kan Shirinta Na Makamashin Nukliya
  • Ibas ya naɗa kantomomin ƙananan hukumomin Ribas