Aminiya:
2025-04-12@07:07:53 GMT

Majalisar wakilai ta dakatar da CBN daga ƙara kuɗin cajin ATM

Published: 12th, March 2025 GMT

Majalisar Wakilai ta umarci Babban Bankin Najeriya (CBN), da ya dakatar da sabon tsarin ƙarin caji kan cire kuɗi ta na’urorin ATM.

Wannan umarni ya biyo bayan wata sanarwa da CBN ya fitar, inda ya ƙuduri aniyar fara cajin Naira 100 kan duk cire Naira 20,000 daga ATM a banki, daga ranar 1 ga watan Maris, 2025.

Hanyoyi 6 da mutum zai kare kansa daga tsananin zafi Zulum ya bai wa ƙananan ’yan kasuwa tallafin 1bn a Borno

Ɗan majalisa Marcus Onobun (PDP, Edo) ne, ya jagoranci ƙudirin da ya buƙaci a dakatar da wannan tsari, inda ya bayyana cewa tsarin zai ƙara jefa ’yan Najeriya cikin wahala.

Ya bayyana cewa, a shekarar 2019, an rage cajin cire kuɗi ta ATM daga Naira 65 zuwa Naira 35, don sauƙaƙa wa al’umma.

Sabon tsarin na CBN ya tanadi cewa, idan kwastoma ya cire kuɗi daga ATM na bankinsa, ba za a caje shi komai ba; amma idan ya cire daga ATM na wani banki daban, za a caje shi Naira 100 kan kowace Naira 20,000 da ya cire.

Majalisar ta nuna damuwa cewa wannan ƙarin caji zai ƙara matsin lamba ga ‘yan Najeriya, musamman ma masu ƙaramin ƙarfi, waɗanda ke fama da hauhawar farashin kayayyaki da sauran matsalolin tattalin arziƙi.

Saboda haka, ta umarci CBN da ya dakatar da aiwatar da wannan sabon tsari har sai an gudanar da cikakken nazari tare da tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin samun mafita mai ɗorewa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Sabon Tsari a dakatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13

Kudin biyan bashin cikin gida na shekarar 2024 ya kai naira tiriliyan 5.97, wanda hakan ke nuna karin kashi 14.15 cikin 100 daga naira tiriliyan 5.23 da aka samu a shekarar 2023. Karuwar ana danganta shi da karuwar kudin ruwa da karin lamuni na cikin gida.

Nijeriya dai ta kashe dala biliyan 4.66 (kwatankwacin naira tiriliyan 7.15 kan farashin canjin naira 1,535.32/$1), wanda hakan ya nuna karuwar kashi 167 cikin 100 daga naira tiriliyan 2.57 da aka samu a shekarar 2023.

Yawan kudin biyan basussuka na waje yana da nasaba da hauhawar farashin ruwa a duniya da kuma faduwar darajar naira, lamarin da ya sa bashin dala ya yi tsada wajen aiki.

Duk da yawan kudin basukan da ke kan Nijeriya, mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gwamnatin tarayya za ta ci gaba da ciwo basuka kadan ta yi amfani da su cikin hanyoyin da suka dace.

Shettima ya bayyana haka ne a karshen makon da ya gabata a Abuja, yayin wani taron da kungiyar akanta ta kasa ta kasa da kuma cibiyar harajin ta Nijeriya ta shirya.

Mataimakin shugaban kasar, wanda ya samu wakilcin mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin tattalin arziki, Dakta Tope Fasua, ya bayyana cewa sannu a hankali ana sake fasalin tsarin karbar basussukan da gwamnati ke yi domin rage bashin.

Ya kuma bayyana cewa, duk da rancen da aka karbo a baya-bayan nan da ya jawo cece-kuce, yanzu Nijeriya na kan hanyar karbar rancen kadan tare da kokarin rage gibin kasafin kudaden da ake fuskanta.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Basukan Da Nijeriya Ke Biya Sun Karu Zuwa Naira Tiriliyan 13
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
  • NAJERIYA A YAU: Tasirin ’Yan Uwantaka Ga Rayuwar Al’umma
  • Trump Ya Dakatar da Harajin Da Sanya Wa Ƙasashen Duniya, Ya Ƙi Cire Wa China
  • Majalisar Kano Ta Yi Murna Da Lambar Yabo Da Jaridar LEADERSHIP Ta Bai Wa Abba
  • Mutanen da suka saba ba ni abinci yanzu na neman taimako — Obi
  • Amurka Ta Ƙara Wa Kayayyakin China Haraji Zuwa Kashi 104
  • Majalisar Jihar Kaduna Ta Bude Bincike Kan Ginin Kasuwa da Aka Yi Watsi da Shi
  • Babu Kuɗin Fansar Da Aka Biya Wajen Ceto Janar Tsiga – DHQ
  • Kotu Ta Daure Ango Kan Liƙi Da Kuɗi A Wajen Bikinsa A Kano