Nazarin CGTN: Manufofin Haraji Na Amurka Sun Rage Kwarin Gwiwa Kan Kasuwar Hannayen Jari Ta Kasar
Published: 13th, March 2025 GMT
Cikin kasa da wata guda, an yi asarar hannayen jari da darajarsu ta kai dala triliyan 4, inda damuwar da duniya ke da shi kan manufofin haraji na Amurka ke haifar da fargaba a kasuwar hannayen jari ta kasar.
Wani nazari da kafar CGTN ta gudanar tsakanin jama’ar duniya masu amfani da intanet ya nuna cewa, mutane na bayyana shakku kan manufofin haraji na sabuwar gwamnatin Amurka, kuma sun damu ainun da mummunan tasirinta kan kasuwar hannayen jari ta kasar dake tafiyar hawainiya.
A baya bayan nan, shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa, “ba zai yuwu mu mayar da hankali sosai kan yanayin kasuwar hannayen jari ba.” A martaninsu, kaso 86.7 na wadanda suka bayar da amsa cikin nazarin, sun yi imanin cewa, wannan wani yunkuri na rage mummunan tasirin da manufofinsa na haraji suka haifar kan kasuwar hannayen jari ta kasar. Har ila yau ba da jimawa ba, shugaba Trump ya sanar da karin haraji kan kayayyakin karafa da gorar ruwa da kasar Canada ke kai wa Amurka, inda ya kara harajin zuwa kaso 50 bisa dari, lamarin da ya kara hargitsa kasuwar hannayen jarin. Don gane da hakan, kaso 86.8 na masu bayar da amsa sun yi ammana cewa, faduwar darajar hannayen jari da aka samu a baya bayan nan a Amurka, ta nuna rashin kwarin gwiwa mai tsanani dake akwai a kasuwar zuba jari a tattalin arzikin Amurka, inda ake kara damuwa cewa, durkushewar kasuwar hannayen jarin ka iya tasiri kan kasuwanni duniya da rage kwarin gwiwa a duniya baki daya.
Nazarin ya gudana ne a dandamalin kafar CGTN na harsunan Ingilishi da Faransanci da Larabci da Rashanci, inda mutane 7,875 suka kada kuri’a tare da bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 24. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasuwar hannayen jari ta kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Tace:Tattaunawa Tare Da Barazana Ba Tattaunawa Ba Ce, Sai Dai Tursasawa
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta bayyana cewa tattaunawa tare da barazana ba tattaunawa ake kiransa ba, sai dai tursasawa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmael Baghaie ya na fadar haka a yau litinin a jawabin mako-makon da ya saba gabatarwa a ko wace ranar litinin.
Baghaei ya kara da cewa JMI ba zata taba tattaunawa da Amurka tare da barazana da kuma takurawa kasar da takunkuman tattalin arziki ba. Zabin tattaunawa ko kuma yaki, ba tattaunawa sai dai tursasawa.
Kafin haka dai shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyana cewa JMI ba ta da zabi, ko ta shiga tattaunawa da Ita Amurka ko kuma ta shiyawa yaki. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen ya kara da cewa takunkuman tattalin arziki mafi muni wanda Amurka ta dorawa kasar tun shekara ta 2018, sun yi illa da kuma tasiri kan rayuwar mutanen kasar Iran, amma wannan bai sa ta mika kai ga bukatun Amurka ba. Ya kuma kara da cewa ko yakin ma, ba zai tilsatawa kasar Iran mika kai ga bukatunta ba.
Abinda Trump yake kira tattaunawa shi ne wakilan kasar Iran su zauna kan wani teburi, sannan Amurka ta ce, ga abinda zaki yi, ga abinda zaki bari, idan kunki yin haka, to ga makamai.
Ya ce, tattaunawa kam, Iran ta yi hakan a yarjeniyar JCPOA kuma an dauki shekaru biyu cur ina tattaunawa tsakanin kasashe 5 +1 da Iran, daga ciki har da ita Amurka.