Yadda Nijeriya Ta Zarce Yawan Man Da OPEC Ta Ware Mata – Bincike
Published: 14th, March 2025 GMT
Sun nuna wannan bukatar ce, biyo bayan hasashen raguwar bukatar Manfetur din da kuma dabarar fitar da shi, daga kasashen da ba sa cikin kungiyar ta OPEC+.
Sai dai, a ranar Litinin da ta gabata kungiyar ta tsaya daram kan tsarinta na kara yawan Man da ake hakowa a watan Afirilu.
Kazalika, binciken na kafar Reuters ya kuma gano yawan adadin karuwar Man na OPEC wanda ya kai Ganguna 80,000 da suke fitowa daga kasar Iran wanda ya kai Ganuna miliyan 3.
Bugu da kari, binciken ya sanar da cewa, fitar da danyan mai daga Iran ya farfado lokacin gwamnatin tsohon shugaban Amurka, Joe Biden duk da takuntuman kasar Amurka, sai da karkashin shugaban kasar Amurka Donald Trump, na sabunta kokarinta.
Sauran Man na biyu na fitowa ne daga Nijeriya, inda yawan Man da take fitawa ya karu kuma yawan bukatarsa a cikin gida ta karu saboda samar da Matatar Mai ta Dangote.
Hakazalika, bincken na kafar Reuters, ya gano cewa, yawan Man da manyan kasasshe biyu da suke a cikin kungiyar OPEC wato Saudi Arabia da Irak, na su ya ragu, inda a yanzu suke hako kasa da wanda OPEC+ ta sanya masu su hako.
A cewar nazarin, man da kasashe mambobin kungiyar OPEC suka fitar a watan Fabrairun 2025 ya karu, inda Iran ke kan gaba, duk da kokarin da kasar Amurka ta yi na yunkurin dakile fitar da man.
To sai dai a ranar Litinin, ta yanke shawarar dakatar da shirin nata, inda take sa ran kara yawan man da take hakowa a watan Afrilu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yawan Man da
এছাড়াও পড়ুন:
Muƙarraban Uba Sani ne suka sace tsohon Kwamishina na – El-Rufai
Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, ya fasa baragurbin ƙwai kan zargin sace Jafaru Sani, tsohon Kwamishina a gwamnatinsa.
El-Rufai, wanda ya mulki Jihar Kaduna daga 2015 zuwa 2023 kafin ya miƙa mulki ga Sanata Uba Sani, wanda shi ne ɗan takarar da ya fi so ya gaje shi, ya bayyana wannan batu ne a shafinsa na Facebook da aka tantance sahihancinsa a ranar Alhamis.
Tsaro: Shugaban Ƙaramar Hukuma ya tabbatar da haɗa kai da Sarakuna Galibin ’yan Najeriya na neman muƙaman gwamnati don arzuta kansu — ObasanjoA cewarsa, an tsare tsohon Kwamishinan na shi ne a kurkuku ba bisa ƙa’ida ba.
El-Rufai ya ce, yana da tabbacin ana cin zarafin abokin nasa ne saboda ya fice daga Jam’iyyar APC zuwa SDP.
“An sace abokin aikinmu kuma tsohon kwamishina mai ƙwazo a zamanin mulkin El-Rufai, Malam Jafaru Sani, an sace shi ne a Kaduna da rana tsaka, yana ta hannun ‘yan fashin dajin Uba Sani da ke cewa su ’yan sanda ne!
“An tsare Jafaru a kurkuku ba tare da wata takardar sammaci daga ‘yan sanda ko ta tuhuma daga Ma’aikatar Shari’a ta Jiha ba.
“Bayan bincike, mun gano cewa ana zarginsa da safarar kuɗi. Amma ainihin laifin Jafaru shi ne ficewarsa daga APC zuwa SDP.
“Wannan salon zaluncin iri ɗaya ne da wanda aka taɓa yi wa wani abokinmu, Bashir Saidu, wanda aka sace a ranar 31 ga Disamba, 2024, aka tsare shi na tsawon kwanaki 50 kafin a bayar da belinsa!
“Rawar da wasu alƙalai ke takawa a shari’ar Kaduna abu ne mai matuƙar damuwa. Muna sa ido kuma muna jira domin babu wani yanayi da zai dawwama, kuma ranar hisabi za ta zo.”
Har yanzu gwamnatin Jihar Kaduna ba ta mayar da martani kan waɗannan zarge-zargen da El-Rufai ya yi ba.