HausaTv:
2025-04-24@23:36:57 GMT

Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza

Published: 16th, March 2025 GMT

Gwamnatin da kuma mutanen kasar Somalia sun ki amincewa da shawarar shugaban kasar Amurka Donal Trump na korar Falasdinawa a Gaza zuwa kasar Somalia.

Shafin yanar Gizo na ‘Africa News’ ya nakalto yan kasar Somalia da dama suna fadar cewa yan kasar da kuma gwamnati ba zasu amince da korar Falasdinawa a Gaza, zuwa kasar Somalia kamar yadda shugaban kasar Amurka Donal Trump yake bada shawara ba.

Mohamed Mohamed Elmi Afrah daya daga cikin mutanen kasar Somalia wanda Shafin labarai na ‘Africa News’ yayi wa tambayoyi danganne da haka, yace: Ban tsamman cewa mutanen kasar Somalia zasu aminjce ba haka ma gwamnatin kasar.

Kafin haka dai wasu da dama suna ganin korar Falasdinawa daga Gaza ra’ayin yahudawan sahyoniyya ne, amma bayan da shugaban kasar Amurka Donal Trump wanda yahudawa suke  jujjuyawa ya gabatar da shi a fadar white House al-amarin ya sami maida martani mai tsananai daga shuwagabannin kasashen duniya. Da kuma kungiyoyin kare hakkin bil’adama.

Trump ta farko ya bada shawarar cewa kasashen Jordan da Masar su karbi mutanen Gaza, da suka ki sai ya koma kan sudan da Somaliya Somali landa da wasu kasashen kamar saudiya da sauransu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: mutanen kasar Somalia

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Yemen Zata Aiwatar Da Abubuwan Mamaki Da Zasu Firgita Makiyanta Kuma Abokan Gaba

Jami’in kasar Yemen ya jaddada cewa: Kwanaki masu zuwa za su aiwatar da abubuwan mamaki da za su ba abokan gabanmu mamaki!

Daraktan sashin yada labarai na fadar shugaban kasar Yemen Zaid Al-Gharsi ya jaddada samun gagarumin ci gaba a karfin sojojin kasar Yemen musamman a fannin fasaha da makamai. Ya yi nuni da cewa, kasar Yemen na gab da samar da sabbin makamai da za su bai wa kowa mamaki.

A cikin wata hira da tashar talabijin ta Al-Alam, Zaid Al-Gharsi ya yi magana game da irin goyon bayan da kasar Yamen ke ba wa yankin Zirin Gaza, inda ya yi nuni da mahimmancin hare-haren soji kai tsaye kan makiya ‘yan sahayoniyya tare da jaddada fifikon karfin kasar Yemen idan aka kwatanta da na ‘yan sahayoniyya da Amurkawa.

Al-Gharsi ya bayyana cewa, yakin da ake yi a halin yanzu yana da manyan fasahohi, saboda makiya ‘yan sahayoniyya sun mallaki fasahar soji na zamani da kuma dogaro da goyon bayan Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • Kasar Yemen Zata Aiwatar Da Abubuwan Mamaki Da Zasu Firgita Makiyanta Kuma Abokan Gaba
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Iran ta jaddada cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Gudanar Da Tattaunawa Kan Tsaronta Ba
  • Dakarun IRGC Suna Cikin Shirin Ko Ta Kwana Don Kare JMI Daga Makiyanta
  • ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso
  • Yakin Ciniki Kalubale Ne Kuma Dama Ce Ga Nahiyar Afirka
  • Mutanen da aka kashe a Binuwai sun ƙaru zuwa 72
  • Yawan mutanen da aka kashe ya ƙari zuwa 72
  • Trump : “Mun yi ganawa mai kyau da Iran”