HausaTv:
2025-03-17@09:42:59 GMT

Gwamnatin Da Mutanen Kasar Somalia Sun Ki Amincewa Da Karban Mutanen Gaza

Published: 16th, March 2025 GMT

Gwamnatin da kuma mutanen kasar Somalia sun ki amincewa da shawarar shugaban kasar Amurka Donal Trump na korar Falasdinawa a Gaza zuwa kasar Somalia.

Shafin yanar Gizo na ‘Africa News’ ya nakalto yan kasar Somalia da dama suna fadar cewa yan kasar da kuma gwamnati ba zasu amince da korar Falasdinawa a Gaza, zuwa kasar Somalia kamar yadda shugaban kasar Amurka Donal Trump yake bada shawara ba.

Mohamed Mohamed Elmi Afrah daya daga cikin mutanen kasar Somalia wanda Shafin labarai na ‘Africa News’ yayi wa tambayoyi danganne da haka, yace: Ban tsamman cewa mutanen kasar Somalia zasu aminjce ba haka ma gwamnatin kasar.

Kafin haka dai wasu da dama suna ganin korar Falasdinawa daga Gaza ra’ayin yahudawan sahyoniyya ne, amma bayan da shugaban kasar Amurka Donal Trump wanda yahudawa suke  jujjuyawa ya gabatar da shi a fadar white House al-amarin ya sami maida martani mai tsananai daga shuwagabannin kasashen duniya. Da kuma kungiyoyin kare hakkin bil’adama.

Trump ta farko ya bada shawarar cewa kasashen Jordan da Masar su karbi mutanen Gaza, da suka ki sai ya koma kan sudan da Somaliya Somali landa da wasu kasashen kamar saudiya da sauransu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: mutanen kasar Somalia

এছাড়াও পড়ুন:

Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington

A ranar Juma’a ce Amurka ta bai wa Jakadan Afirka ta Kudu, Ebrahim Rasool, wa’adin sa’o’i 72 ya tattara komatsai ya fice daga ƙasar.

Hakan na kunshe cikin wata ’yar takaitacciyar sanarwa da mai magana da yawun ma’iakatar harkokin wajen Amurka, Chrispin Phiri ta fitar.

Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio ya zargi Ebrahim Rasool da kasancewa “dan siyasar wariyar launin fata mai kyamar Amurka,” lamarin da ya kara rura wutar rikicin diflomasiyya da ya kunno kai tsakanin Washington da Pretoria.

A cikin watan Fabarairun da ya gabata ne Shugaba Donald Trump ya wallafa wani saƙo a shafinsa na sada zumunta na Truth Social cewa Amurka ta dakatar da duk wani tallafi da take bai wa Afirka ta Kudu, sakamakon zarginta da ƙwace gonakin fararen fata na ƙasar.

Wannan dalili ne ya sa shugaba Trump ya sanar da cewa duk wani manomi da aka kwace wa gona, kuma yake fatan koma wa Amurka to zai samu izinin zama ɗan ƙasar cikin sauƙi.

Matakin da Amurka ta dauka na korar jakadan Afirka ta Kudu “abin takaici ne,” kamar yadda ofishin shugaban ƙasar Cyrill Ramaphosa ya bayyana a ranar Asabar, yana mai kira ga “gyara diflomasiyya” tsakanin kasashen biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Adadin Shahidan Falasdinawa A Gaza Ya Karu Da 14 A Jiya Lahadi Saboda Hare-Haren Sojojin HKI
  • Iran Ta Yaba Da Yarjeniyar  Zaman Lafiya Da Aka Cimma Tsakanin Kasashen Armenia Da Azerbaijan
  • Afirka Ta Kudu Ta Caccaki Amurka Kan Korar Jakadanta Daga Washington
  • Hizbullah ta yi Allah wadai da harin Amurka da Birtaniya a kan Yemen
  • Kofar JMI A Bude Take Don Tattaunawa Da Kasashen Turai
  •  Pakistan Ta Zargi Kasashen Afghanistan Da India Da Hannu A Garkuwa Da Jirgin Kasa Na Sojoji
  • Nageriya ta Maida Martani Kan Zargin Kissin Kiristoce A Kasar,Wanada Gwamnatin Amurka Ta Yi Mata
  • Amurka Ta Ce Bata Bukatar Jakadan Kasar Afirka Ta Kudu A Kasar, Bayan Da Ya Aibata Shugaba Trump
  • Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba